Tinubu ya isa Kigali domin halartar taron ƴan kasuwa da masu zuba jari na Afrika

Asalin hoton, Bayo Onanuga
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya isa birnin Kigali na ƙasar Rwanda domin halartar taron ƴan kasuwa da masu zuba jari na Afrika da ake kira da Africa CEO Forum karo na 13, wanda zai fara a ranar Alhamis.
An tarɓi Shugaba Tinubu a filin jirgin saman Kigali inda Ministan Harkokin Waje, Ambasada Bianca Ojukwu da Ministan Tsaron Rwanda, Juvenal Marizamunda suka tarbe shi.
Sauran da suka halarci tarbar sun haɗa da ministar masana’antu, kasuwanci da Zuba Jari, Dr Jumoke Oduwole da daraktan hukumar tsaron ƙasa (NIA) da Ambasada Mohammed Mohammed, da kuma wakilin Najeriya a Rwanda, Ambasada Ibrahim Zanna.
Taron wanda aka kafa a shekarar 2012 shi ne babban taron shekara-shekara da ke tattaro shugabannin kamfanoni, masu zuba jari da masu tsara manufofi a Afrika.
Taron na mayar da hankali ne kan inganta ci gaban tattalin arziki ta hanyar haɗin gwiwa, haɗa kasuwanni da ƙarfafa zuba jari tsakanin ƙasashe.
A yayin taron, Shugaba Tinubu zai gabatar da jawabi inda zai bayyana nasarorin da ake samu daga sauye-sauyen tattalin arzikin Najeriya.
Haka kuma, ana sa ran Tinubu zai gudanar da tarurruka da manyan shugabannin kasuwanci daga Afrika da sauran sassan duniya.









