KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Alhamis 14//05/2026

  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, da Usman Minjibir da Aisha Babangida

  1. Wani jigo a gwamnatin Birtaniya ya aje muƙaminsa

    Birtaniya

    Asalin hoton, PA Media

    Sakataren lafiya na Birtaniya Wes Streeting ya ce baya da ƙwarin gwiwa kan shugabancin Firaministan ƙasar Keir Starmer, wanda a cewarsa hakan ya sa ya ajiye muƙamin.

    A cikin takardar ajiye aiki da ya rubuta Mr Wes ya ce ƙasar na buƙatar hangen nesa a maimakon barin giɓi. Ya dauki matakin ne bayan da sakamakon zaɓen da ya gabata bai yi ma jam'iyar Labour dadi ba.

    Sai dai a cikin takardar ta shi bai nuna wata alama da ke nuna kai tsaye yana goyon bayan Starmer ya sauka daga muƙaminsa ba.

    Wakilin BBC ya ce dukkaninmu mun san cewa yana shirin shiga cikin masu son shugabanci, babban abinda yafi jan hankali a cikin takardar da ya rubuta shine ya ce ƙasar na fuskantar babban kalubale.

  2. Shin China na taka muhimmiyar rawar bayan fage a rikicin Iran?, Anthony Zucker da Laura Baker - BBC

    China

    Asalin hoton, EPA

    Ziyarar da ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya kai birnin Beijing a makon da ya gabata ta ƙara fito da irin tasirin da China ke da shi a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Rahotanni sun nuna cewa Amurka na sanya ido sosai kan wannan al’amari, musamman dangane da yadda China ke hulɗa da Iran a lokacin da rikici ke ƙaruwa a yankin.

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce yana fatan China za ta faɗa wa Iran abin da ya kamata ta sani.

    “Ina fatan China za ta gaya masa abin da ya kamata a faɗa, wato abin da suke yi a mashigar Hormuz ya sa duniya ta ware su. Su ne ake gani a matsayin masu laifi a wannan rikicin,” in ji Rubio.

    Shi ma Ali Wine, babban mai ba da shawara kan hulɗar Amurka da China a ƙungiyar International Crisis Group, ya ce Amurka ta fahimci cewa China za ta taka muhimmiyar rawa idan ana son dawo da Iran teburin tattaunawa cikin hanya mai ɗorewa.

    “Ina ganin Amurka ta fahimci cewa idan ana son dawo da Iran kan teburin sulhu ta hanya mai ɗorewa na dogon lokaci, to lallai China za ta taka rawa,” in ji shi.

    A nasa ɓangaren, shugaban Amurka Donald Trump ya nuna kamar ba ya damuwa sosai da kusancin da ke tsakanin China da Tehran.

    Ko da yake Amurka ta kakaba wa wani matatar mai da ke China takunkumi saboda safarar man Iran, Trump ya rage muhimmancin duk wata goyon bayan da China ke bai wa Iran yayin rikicin.

  3. Makinde ya yanki takardar tsayawa takarar shugaban Najeriya

    ....

    Asalin hoton, @seyimakinde/X

    Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya ayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban Najeriya a zaɓen shekarar 2027, inda ya bayyana cewa zai nemi kujerar ne ƙarƙashin jam’iyyar Allied Peoples Movement (APM).

    Ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin wani babban gangamin haɗakar jam’iyyun PDP da APM da aka gudanar a Ibadan.

    Sanarwar ta Makinde ta ja hankalin dubban magoya baya da masu ruwa da tsaki da kuma abokan siyasarsa, lamarin da masana ke gani a matsayin wani muhimmin mataki a sauye-sauyen siyasa da ke ci gaba da faruwa gabanin babban zaɓen gaba.

    Sanarwar tasa dai na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun shirye-shiryen siyasa gabanin zaɓen 2027, inda masana ke ganin matakin na iya sauya yanayin siyasar ƙasar, musamman a yankin Kudu maso Yamma.

  4. 'Iran na bai wa jiragen China damar wucewa ta mashigar Hormuz'

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni na cewa Iran ta bai wa ƙarin jiragen ruwan ƙasar China damar wucewa ta mashigar Hormuz tun daga daren jiya.

    Kamfanin dillancin labarai na Fars, wanda ya ambato wata majiya mai tushe, ya ce an ɗauki matakin ne bayan buƙatun da ministan harkokin wajen China da kuma jakadan Beijing da ke Iran suka gabatar.

    Fars ta ce a cikin kwanakin nan, aƙalla jiragen dakon mai da manyan jiragen ruwa guda shida mallakin China ko masu aiki da ita sun ratsa mashigin Hormuz.

    Sashen bincike na BBC Verify ya kuma tabbatar da cewa aƙalla wani babban jirgin dakon mai na China ya bi ta mashigar Hormuz a jiya.

    Babban jirgin mai mai suna Yuan Huahu, wanda ke ɗauke da tutar China, ya tsaya a Basra da ke Iraq a farkon watan Maris inda ya ɗauki kayan mai, kamar yadda bayanan siginar motsinsa suka nuna.

    Rahotanni sun ce jirgin ya ratsa mashigar Hormuz da sanyin safiyar Laraba 13 ga watan Mayu, inda ya bayyana matsayinsa na kusan minti 90 kacal a ruwan Iran kusa da tsibirin Lark.

    Daga baya, bayan fiye da sa'o'i 12, jirgin ya sake bayyana matsayinsa yayin da yake tsakiyar Tekun Oman gabashin birnin Sohar na ƙasar Oman, a cewar BBC.

    An bayyana cewa jirgin na kan hanyarsa ta zuwa tashar jiragen ruwa ta Zhoushan da ke China, inda ake sa ran zai isa a farkon watan Yuni.

    Har zuwa yanzu dai hukumomin China ba su tabbatar da wannan rahoto ba.

  5. Manyan ƙalubale da ke hana matasa yin takara a Najeriya

    ..

    Asalin hoton, NotTooYoungToRun

    Duk da cewa tsohon shugaban Najeriya, marigayi Muhammadu Buhari ya saka hannu a dokar da ta bai wa matasa damar tsayawa takara a 2018, amma har yanzu masu karancin shekaru na fuskantar tarnaƙi iri-iri a siyasa ƙasar.

    A duk lokacin da zaɓe ya ƙarato a Najeriya, ana ganin matasa ne suka fi cika filayen yaƙin neman zaɓe da tarukan siyasa - su ne ke liƙa fastoci da yaɗa saƙonni a kafafen sada zumunta da kuma zagaya unguwanni suna neman ƙuri'u domin 'yan takara.

    To amma idan aka duba cikin jerin masu neman kujerun siyasa, sai a tarar cewa matasa kaɗan ne ke samun damar shiga takara.

    Wannan lamari ya daɗe yana jawo muhawara a tsakanin al'umma, musamman ganin cewa matasa su ne mafi rinjaye a Najeriya.

    Duk da yawan kiraye-kirayen da ake yi na bai wa matasa dama a shugabanci, har yanzu da yawa daga cikinsu na kallon siyasa a matsayin wata hanya mai cike da wahala, kuɗi da kuma tasirin masu ruwa da tsaki.

  6. 'Ba makawa kan ƙara farashin tikitin jirgin sama a Turai'

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Ƙungiyar kula da sufurin Jiragen Sama ta Duniya ya yi gargaɗin cewa babu makawa kan batun ƙarin farashin tikitin jiragen sama a Turai saboda tsadar man jiragen sama da yaƙin Iran ya haddasa.

    Willie Walsh ya shaida wa BBC cewa ko da za a kawo ƙarshen yaƙin gobe, tasirinsa kan masana'antar sufurin jiragen sama zai ci gaba har cikin watanni masu zuwa.

    Ya ce idan har ba a samu wata kafar samar da isasshen man ba, za a iya fuskantar tsaiko idan aka shiga watannin bazara na Yuni da Yuli da kuma Agusta.

    Ƙasashen Turai, da Birtaniya, sun dogara ne kacokan kan shigo da mai daga Gabas ta Tsakiya, wanda a halin yanzu ba su iya samu sakamakon datse mashigar Hormuz.

  7. Tsawa da ruwan sama sun yi ajalin fiye da mutum 100 a Indiya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Tsawa da ruwan sama mai ƙarfi sun halaka aƙalla mutum fiye da 100 a jihar Uttar Pradesh da ke arewacin Indiya.

    Wani jami'i daga hukumar kare bala'oi ya ce sama da mutum 50 sun jikkata sannan lamarin ya yi ɓarna a gidaje da dama da ke gundumomi.

    An samu mutane da dama da lamarin ya rutsa da su sakamakon rushewar bango da faɗuwar bishiyoyi da kuma tsawa.

    Masu hasashen yanayi sun yi gargaɗin za a iya samun tsawa a sassan arewacin Indiya a ƴan kwanaki masu zuwa.

  8. Dizel da man fetur sun ƙare a Cuba - ministan makamashi

    ...

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Ministan makamashi a Cuba ya ce dizel da man fetur sun ƙare gaba ɗaya a ƙasar.

    A wata hira da ya yi da kafar yaɗa labarai a ƙasar, Vicente de la O Levy ya ce akwai ƙarancin gas kasancewar makamasshin Cuba yana cikin garari sakamakon toshe zirga-zirga a mashiar Hormuz.

    A ranar Laraba ne zanga-zanga ta ɓarke kan rashin wuta a Havana, babban birnin ƙasar, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

    A makon nan ne Amurka ta jaddada tayin tura dala miliyan 100 zuwa ƙasar don zama musaya na gyare-gyare masu muhimmanci na tsarin kwamunisanci na Cuba.

    Asibitoci sun shiga wani hali yayin da lamarin ya tilasta rufe makarantu da ofisohin gwamnati. Kazalika, halin da ake ciki ya yi tasiri kan al'amuran yawon buɗe ido wanda ya sakance babbar hanyar samun kuɗi ga Cuba.

    Cuba ta dogara kan Venezuela da Mexico domin samun mai sai dai ƙasashen biyu sun daina samar da man tun bayan da Shugaba Donald Trump ya yi barazanar ƙaƙaba haraji kan ƙasashen da suka kuskura suka tura mai zuwa Cuba.

  9. Dangote ya yi watsi da tayin NNPC na ƙara hannun jari a matatarsa

    Dangote

    Asalin hoton, EPA/Shutterstock

    Shugaban Kamfanin Dangote, Aliko Dangote ya ce kamfaninsa ya yi watsi da buƙatar da kamfanin mai na Najeriya NNPC ya gabatar ta neman ƙara yawan hannun jarinsa a matatar man Dangote da kashi 7.25 cikin 100.

    Dangote ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da shugaban asusun zuba jari na Norway, Nicolai Tangen.

    Jaridar Punch ta ruwaito cewa an samu ƙaruwar man da ake tacewa a matatar mai da ke Lekki zuwa lita biliyan 3.18 a watanni uku na farkon 2026 yayin da man da ake shigowa da shi ya ragu sosai da lita miliyan 965.52.

    Binciken da aka ƙara yi ya nuna cewa yaƙin Amurka da Iran da ya janyo matsalar mai ya haifar da ƙaruwar kuɗin shiga ga matatar Dangote yayin da matatar ta ƙara yawan tataccen man da take fitarwa.

    A cewar Dangote, an ƙi amincewa da tayin NNPC na ƙara kashi 7.25 na hannun jarinsa a matatar saboda kamfanin yana shirin bai wa sauran ƴan Najeriya damar zuba hannun jarinsu a kamfanin.

  10. Shugaba Ramaphosa zai je majalisa don amsa tambayoyi

    Shugaba Cyril Ramaphosa

    Asalin hoton, Ziyaad Douglas/Gallo Images via Getty Images

    Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa zai bayyana gaban majalisar dokoki a yau inda ake sa ran zai fuskanci matsin lamba daga ƴanmajalisa na ɓangaren hamayya.

    Wannan ne karon farko da Shugaba Ramaphosa zai fuskanci ƴanmajalisa tun bayan da wata kotu a ƙasar ta yanke cewa ya kamata majalisar ta fara shiri kan ko za a tsige shugaban.

    A cewar kafar yaɗa labarai ta SABC, ba lalle a tado da batun Kotun Tsarin mulkin ba sai dai wasu ƴanmajalisar na ɓangaren hamayya za su iya taɓo batun.

    Ramaphosa zai yi magana ne kan ayyukan soji na kakkaɓ yankuna daga masu aikata miyagun laifuka da kuma wuraren da ake haƙon ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba.

    Zai kuma yi magana kan hanyoyin da ya bi na dakatar da kwamishinan ƴansanda, Fannie Masemola da kuma abin da gwamnatinsa take yi game da ƙaruwar rashin ayyukan yi.

  11. An zaƙulo matattu daga ɓuraguzai a Kyiv

    ...

    Asalin hoton, Andrew Kravchenko / Bloomberg via Getty Images

    Jami'ai a Kyiv sun ce an zaƙulo gawawwakin mutum uku daga ɓuraguzan ginin da Rasha ta kai wa hari a Kyiv inda ake ci gaba da aikin ceto sakamakon ɓarnar da hare-haren suka yi.

    Aƙalla mutum 144 ne suka ji rauni har da yara biyu, in ji magajin garin. 21 cikinsu suna samun kulawa a asibiti, har da yaro guda.

    Rana ta uku ne nan da Ukraine ke bayar da rahoton mace-mace yayin da Rasha ke zafafa hare-hare bayan da yarjejenyar tsagaita wuta ta ƙare ranar Litinin.

    A hare-haren na cikin dare, an harba fiye da jirage marasa matuƙa 670 sai makamai masu linzami 56 zuwa sassan Ukraine, kamar yadda Shugaba Volodomyr Zelensky ya bayyana.

  12. 'Bakin Amurka da China ya zo ɗaya kan hana Iran mallakar makamin nukiliya'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Fadar White House ta ce Shugaba Trump da takwaransa na China, Xi - da ke ganawa a Beijing - sun amince cewa bai kamata Iran ta mallaki makamin nukiliya ba kuma ya zama dole a buɗe Mashigar Hormuz.

    Wata sanarwa daga Amurka game da ganawar ta tsawon sa'a biyu ta ce akwai fahimtar juna tsakaninsu kuma shugabannin biyu suna aiki don inganta alaƙarsu ta tattalin arziki sai dai sanarwar ba ta ambaci ɗaya daga cikin batutuwan da suke taƙaddama a kai ba - Taiwan.

    Mista Xi ya ce ya kamata Amurka da China su zama "abokan hulɗa ba abokan gaba ba" sai dai ya yi gargaɗin za a iya samun saɓani kan maganar Taiwan.

  13. NEMA ta buƙaci jihohi su ɗauki matakan kariya daga ambaliya

    Shugabar Hukumar NEMA

    Asalin hoton, @nemanigeria

    Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya ta yi kira ga gwamnonin jihohi da u fara ɗaukan matakan riigakafi da nufin kaucewa matsalar ambaliya sakamakon hasashen da aka yi cewa fiye da jihohi 30 na iya fuskantar gagarumar matsalar ambaliya a daminar bana.

    A cewar saƙon da NEMA ta wallafa a shafinta na X, Shugabar hukumar Zubaida Umar ta yi kira ga jihohin da su gaggauta ɗaukan mataki domin rage tasirin ambaliyar da aka yi hasashen za a samu a wasu yankunan ƙasar.

    Sanarwar ta ce wasu daga cikin matakan da ake tsammanin jihohin su ɗauka sun haɗa da sake farfaɗo da shirin tsaftar muhalli duk wata da yawan gyara magudanan ruwa da hanyoyin wucewar ruwa.

    Shugabar NEMA ta kuma ce yi kira ga sarakunan gargajiya da malaman addini da ƙungiyoyin matasa da kafafen yaɗa labarai da kamfanoni masu zaman kansu da su tallafa wa ƙoƙarin hukumar wajen kare afkuwar ambaliya a ƙasar

  14. ‘Netanyahu bai ziyarci Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa a asirce ba’

    Netanyahu

    Asalin hoton, Reuters

    Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta musanta cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya kai wata ziyarar sirri ƙasar, duk da cewa ofishin Mista Netanyahu ya sanar da ziyarar ne sa'o'i kaɗan kafin hakan.

    Wakiliyar BBC ta ce Ma'aikatar harkokin wajen haɗaɗɗiyar daular larabawar ta musanta batun ziyarar da kakkausar murya inda ta ce dangantaka da Isra'ila a fili ake gudanar da ita kuma duk wani iƙirari game da ziyarar da ba a sanar ba "ba ta da tushe.

    Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta kasance ɗaya daga cikin ƙasashen Larabawa da dama da suka ƙulla hulɗar jakadanci da Isra'ila bayan yarjejeniyar Abraham Accords a wa'adin shugabancin Trump na farko.

  15. Ana laluben mutanen da suka mutu bayan harin Rasha a Kyiv

    Masu aikin ceto

    Asalin hoton, Reuters

    Magajin garin Kyiv ya ce Rasha ta kai wani gagarumin hari ta sama kan babban birnin na Ukraine kuma tuni jami'ai suka duƙufa domin duba ɓuraguzai don zaƙulo waɗanda lamarin ya rutsa da su.

    Lamarin ya yi ajalin mutum biyu sai wasu 40 da suka ji rauni kamar yadda jami'ai suka bayyana.

    Vitaliy Klitschko, wanda ya ziyarci ginin da lamarin ya shafa, ya ce lamarin ya shafi ɗakuna 18.

    A cewar shi, harin ya lalata hanyoyin samar da ruwa na birnin.

    A ranar Laraba Rasha ta kai hari mafi girma da aka kai ta sama kan Ukraine tun bayan fara yaƙi tsakanin ƙasashen.

    Shugaba Zelensky ya ce Moscow ta harba wasu jiragen sama marasa matuƙa sama da ɗari takwas kuma tuni aka kuɓutar da mutane gommai daga ginin.

  16. Ministan harkokin wajen Iran ya halarci taron BRICS a Indiya

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya isa ƙasar Indiya domin halartar taron ministocin harkokin wajen ƙasashen BRICS.

    Yayin wannan ziyara, ana sa ran Mista Araghchi zai gana tare da tattaunawa da takwarorinsa daga sauran ƙasashe yayin da yake halartar taron.

    Rahotanni sun ce yaƙin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran shi ne babban abin da ke jan hankali a tattaunawar da mambobin ƙungiyar ke yi.

    Ana gudanar da taron ministocin harkokin wajen BRICS na kwanaki biyu ne a birnin New Delhi na ƙasar Indiya.

    BRICS ƙungiya ce da ta ƙunshi manyan ƙasashe masu tasowa a duniya. Brazil da Rasha da Indiya da China da kuma Afirka ta Kudu su ne manyan mambobin ƙungiyar. Sunan BRICS ya samo asali ne daga haruffan farko na sunayen ƙasashen a harshen Igilishi.

    Iran ta zama cikakkiyar mamba a ƙungiyar shekaru biyu da suka gabata.

  17. Jami'an kwastam biyu sun mutu a fafatawa da Lakurawa

    Shugaban hukumar kwastam, Bashir Adeniyi

    Asalin hoton, Nigeria Customs Service/Facebook

    Jami'an hukumar kwastam biyu sun rasa ransu a fafatawar da suka yi da mayaƙan da ake zargi Lakurawa ne a jihar Kebbi.

    Shugaban hukumar kwastam, Bashir Adeniyi, ya ce lamarin ya faru ne da safiyar ranar Laraba.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa jami'an masu muƙamin ASC da DSC, sun rasa ransu ne yayin samamen yaƙi da ƴan ta'adda da tsakiyar dare.

    Adeniyi ya faɗi hakan ne a birnin Illorin yayin da yake gabatar da jawabi a jami'ar Illorin da ke jihar Kwara.

    Rahotanni sun ce maharan sun farwa shingen binciken ababen hawa na tsaro da ke kusa da juna.

    A nan ne kuma suka harbi jami'i guda sannan suka cinna wa ɗaya jami'in wuta da ransa.

    Gwamnan jihar Kwara, AbdurRahman AbdulRazaq ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga hukumar ta kwastam kan mutuwar jami'an biyu inda ya bayyana su a matsayin ƴan kishin ƙasa da suka rasa ransu yayin hidimta wa ƙasarsu.

  18. Indiya ta gargaɗi duniya kan rikice-rikicen da ke girgiza tattalin arziki

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Ministocin harkokin wajen ƙasashen BRICS ciki har da Iran da Rasha sun gana a birnin New Delhi na ƙasar Indiya, inda gwamnatin Indiya ta bayyana damuwa kan yadda rikice-rikice ke ƙara jefa duniya cikin rashin tabbas a tattalin arziki da harkokin makamashi.

    Yaƙin Iran da matsalar man fetur da ta biyo baya sun mamaye muhawarar taron na kwanaki biyu.

    A jawabin buɗe taron, ministan harkokin wajen Indiya, Subrahmanyam Jaishankar, ya ce duniya na cikin wani yanayi mai cike da sauye-sauye da tashin hankali a dangantakar ƙasa da ƙasa.

    Ya ce rikice-rikice, matsalolin tattalin arziki, ƙalubalen kasuwanci da fasaha, da kuma sauyin yanayi na ci gaba da sauya tsarin duniya.

    Jaishankar ya ƙara da cewa ƙasashe masu tasowa na sa ran BRICS za ta taimaka wajen samar da kwanciyar hankali da daidaito a duniya.

    Haka kuma ya ce ƙasashe da dama har yanzu na fuskantar matsaloli da suka haɗa da tsaron makamashi, samar da abinci da taki, harkokin lafiya da kuma samun kuɗaɗen tallafi.

  19. Ya kamata Amurka da China su zama abokan hulɗa ba na hamayya ba - Xi Jinping

    Shugaba Trump da Xi Jinping

    Asalin hoton, VGC via Getty Images

    Shugaba Xi Jinping na China ya shaida wa Donald Trump cewa, kamata ya yi ƙasashensu su kasance abokan hulɗa, ba abokan hamayya ba, a farkon tattaunawar shugabannin biyu a birnin Beijing.

    Shugaba Trump ya ce a yanzu dangantakar da ke tsakanin manyan ƙasashen biyu za ta inganta fiye da kowane lokaci a tarihi.

    Ya ce abin da mutane ba su sani ba shi ne duk lokacin da aka samu matsala muna warware ta cikin sauƙi kuma za mu ci gaba da tabbatar da danƙon zumuncin da ke tsakanin mu.

    Mista Trump yana tafiya ne tare da wata babbar tawaga da ta ƙunshi manyan jami'an gwamnati da shugabannin kamfanonin fasaha da suka haɗa da Elon Musk da kuma shugaban kamfanin Nvidia Jensen Huang.

  20. Barka da Safiya

    Shafin Kai Tsaye na BBC Hausa na yi wa ɗumbin masu kasancewa da mu barka da wannan lokaci.

    Da fatan an wayi gari cikin ƙoshin lafiya. Kamar kodayaushe, a yau ma za mu ci gaba da kawo maku rahotanni na abubuwan da suka shafi yaƙin Iran da labaran da suka danganci Najeriya da sauran ƙasashen duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labarai da ma kallon bidiyo.