Amurka ce ke da alhakin hare-haren Isra’ila a ƙasarmu - Iran

Asalin hoton, Tasnim news agency
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqaei, ya ce Amurka ce ke da alhakin hare-haren da Isra’ila ta kai wa Iran.
Da yake magana a taron manema labarai na mako-mako, Baqaei ya bayyana cewa duk wani abu da ya faru a yankin, to Amurka ce za ta ɗauki alhakin hakan.
“Duk abin da ya faru a yankin, ko Amurka da kanta ce ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta ta hanyar kai hare-hare kan jiragen kasuwancin Iran da kutsawa yankunan kudancin kasar da dai sauransu, Amurka ce ke da alhaki kai tsaye.
Haka kuma sakamakon duk wani ƙarin tashin hankali zai rataya a wuyanta.”
Bayan hare-haren da Isra’ila ta kai a daren jiya, jami’an Amurka sun bayyana cewa sojojin Amurka ba su da hannu a harin.
Sai dai Baqaei ya ce rundunar sojojin Amurka ta CENTCOM tana aiki tare da Isra’ila a ɓangarorin kai hari da kuma kariya.
Da aka tambaye shi game da rahotannin da ke cewa an kai hari sansanin sojin Yarima Sultan da ke Saudiyya, Baqaei ya ce rundunar sojin Iran kan sanar a hukumance duk wurin da ta kai hari.














