Jam'iyyar APC na gudanar da zaɓen fitar da gwanin shugaban ƙasa

Asalin hoton, Multiple
A yau ne jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ke gudanar da zaɓen fitar da gwanin takarar shugaban ƙasar, domin zaɓen mutumin da zai tsaya mata takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Za a gudanar da zaɓen ne ta hanyar ƴartinƙe kamar yadda jam'iyyar ta tsara.
Cikin sanarwar zaɓen da ta fitar, APC ta ce ta tsara gudanar da zaɓen ne bayan kammala na gwamnoni da na ƴan majalisun tarayya.
Mutum biyu ne ke fafatawa a zaɓen na yau, wato Shugaba Bola Tinubu da ke neman wa'adin mulkin na biyu, sai kuma Stanley Osifo da ke ƙalubalantarsa.
Daraktan yaɗa labaran sakatariyar jam'iyyar, Mallam Bala Ibrahim ya ce za a gudanar da zaɓukan a duka mazaɓun ƙasar.


