KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 23/05/2026

Wannan shafi labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 23/05/2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Jam'iyyar APC na gudanar da zaɓen fitar da gwanin shugaban ƙasa

    Stanley Osifo da Bola Tinubu

    Asalin hoton, Multiple

    A yau ne jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ke gudanar da zaɓen fitar da gwanin takarar shugaban ƙasar, domin zaɓen mutumin da zai tsaya mata takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

    Za a gudanar da zaɓen ne ta hanyar ƴartinƙe kamar yadda jam'iyyar ta tsara.

    Cikin sanarwar zaɓen da ta fitar, APC ta ce ta tsara gudanar da zaɓen ne bayan kammala na gwamnoni da na ƴan majalisun tarayya.

    Mutum biyu ne ke fafatawa a zaɓen na yau, wato Shugaba Bola Tinubu da ke neman wa'adin mulkin na biyu, sai kuma Stanley Osifo da ke ƙalubalantarsa.

    Daraktan yaɗa labaran sakatariyar jam'iyyar, Mallam Bala Ibrahim ya ce za a gudanar da zaɓukan a duka mazaɓun ƙasar.

  2. An samu ɓullar Ebola a lardunan da ake rikici a DR Congo

    Ebola

    Asalin hoton, Getty Images

    Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo ta ce yanzu haka an samu rahoton ɓullar cutar Ebola a wasu lardunan gabashin ƙasar da ke fama da rikici.

    Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce yana da muhimmanci a iya gano waɗanda ake zargin sun kamu da cutar.

    Wani jami'in hukumar mai kula da nahiyar Afirka, Otim Patrick Ramadan ya ce ana samun ƙaruwa adadin waɗanda ake tunanin suna ɗauke da cutar, kuma hakan abu ne mai kyau, saboda yana bayar da damar a hana cutar yaɗuwa a cikin al'umma.

    Sama da mutum 700 ne suka kamu da cutar ta Ebola, yayin da sama da mutum 170 suka mutu.

  3. Shugaban Senegal ya sallami firaministan ƙasar Ousmane Sonko

    .

    Asalin hoton, .

    Shugaban ƙasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye ya sallami firaministan ƙasar, Ousmane Sonko bayan shafe tsawon watanni ana takun saƙa tsakanin mutanen biyu.

    Matakain korar wanda aka bayyana ta gidan talbijin na ƙasar, na zuwa ne bayan zazzafar muhawarar da aka yi a majalisar dokokin ƙasar, inda firaministan ya fito fili ya soki shugaba Faye.

    Da ya ke martani kan sallamar tasa, Mista Sonko ya wallafa saƙo a shafinsa na sada zumunta, inda ya ce yau zai yi barci cikin natsuwa a gidansa.

    Jagororin biyu sun riƙa samun saɓani kan abubuwa da dama masu alaƙa da gwamnati da kuama aƙida.

    A baya-bayan nan dai Mista Sonko ya yi nuni da yiwuwar komawa jam’iyyar adawa, lamarin da masu sharhi ke ganin wani mataki ne na tsayawa takara a zaɓen shugaban ƙasa na 2029.

    A shekarar 2024 ne Mista Sonko, wanda ke samun goyon bayan matasan ƙasar a lokacin, ya zaɓi Faye a matsayin wanda zai tsaya takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar adawa ta lokacin a madadinsa kasancewar an haramta masa tsayawa takara.

  4. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku ci gaba da bibiyarmu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan abaran da muke wallafawa.