UAE ta ayyana harin da aka kai kusa da cibiyar nukiliyarta a matsayin 'ta'addanci'
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta bayyana harin da aka kai da jirage marasa matuka a kusa da tashar makamashin nukiliyarta da ke Barakah a matsayin "aikin ta'addanci ne na rashin hankali" wanda zai ƙara dagula lamura a yankin.
Ma'aikatar harkokin wajen UAE ta yi Allah-wadai da harin "da kakkausar murya" a cikin wata sanarwa da ta fitar, tare da jaddada cewa tana da 'yancinta na diplomasiyya da na soja na mayar da martani ga duk wata barazana.
Sanarwar da Ma'aikatar Harkokin Wajen ta fitar ba ta ambaci daga inda harin ya fito ba, amma ta ce harin ya faɗa kan wani injin janerata da ke wajen cibiyar makamashin nukiliyar ta Barakah da ke yankin Dhafra, kuma jirgi mara matukin ya fito ne daga kan iyakar yammacin ƙasar.
Ana samun tankiya tsakanin Iran da UAE a ƴan kwanakin nan.
UAE ta bayyana cewa Iran ta kai hare-hare sama da 3,000 kan cibiyoyinta da wuraren farar hula a yaƙin da take yi da Amurka da Isra'ila.













