KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Talata 19/05/2026

  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba da Usman Minjibir

  1. Ɗanbindiga ya halaka mutum takwas a Al Ƙahira

    Wani ɗanbindiga ya halaka mutum takwas tare da raunata mutum biyar a Lardin Asyut da ke kudancin Al Ƙahira da ke Masar.

    Ɗanbindigar wanda ya kai harin na ranar Litinin, kamar yadda rahotanni suka cem ya buɗe wuta a wani wata cibiyar sufuri.

    Ma'aikatar harkokin wajen ƙasar ta ce jami'an tsaro sun gano mutumin bayan ya tsere zuwa wata gona inda suka harbe shi sakamakon musayar wuta.

  2. Hisbah ta kama wani kan zargin 'yin soyayya' da matar aure

    Jami'an hukumar Hisbah a jihar Kebbi sun cafke wani mutum da ya ɓuya cikin jakar Ghana Must Go a gidan wata matar aure a yankin Badariya a Birnin Kebbi.

    Daraktan shari'a a hukumar, Sirajo Kamba ne ya tabbatar da kame mutumin a wata sanarwa, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    A cewar Kamba, mazauna yankin sun ankarar da Hisba ne a ranar 18 ga watan Mayu bayan da suka gano wani mutum yana shiga gidan matar.

    "Mazauna unguwar sun yi zargin akwai mu'amalar da ta saɓa shari'ar musulunci tsakanin mutanen biyu, abin da ya sa suka sanar da hukuma.

    "Da samun rahoton ne kuma, hukumar Hisba ta jihar Kebbi ta aike da jami'anta zuwa gidan matar.

    Daraktan ya ce a lokacin da jami'an suka isa gidan, sun nemi su yi bincike a gidan sai dai matar ta ƙi bayar da dama inda ta musanta cewa babu kowa a cikin gidan.

    Daraktan ya kuma ce daga bisa ni ne matar ta amince a yi bincike lamarin da ya sa aka gano wanda ake zargi cikin wata jakar Ghana Must Go.

    Ya ƙara da cewa binciken da aka zurfafa ya nuna cewa akwai alaƙa ta soyayya tsakanin matar mai aure da kuma mutumin.

    Kamba ya ce masoyan sun tabbatar da zargin da ake musu inda ya ce za a gurfanar da su gaban kotu domin fuskantar shari'a bisa tanadin musulunci.

  3. Na janye ƙudirin sake kai wa Iran hari saboda ƙasashen Gulf - Trump

    ..

    Asalin hoton, EPA/Shutterstock

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya janye ƙudirin kai wa Iran hari jiya Talata saboda ƙasashen yankin Gulf sun buƙaci hakan yayin da ake muhimmiyar tattaunawar sulhu.

    A wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, Trump ya ce shugabannin Qatar da Saudiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ne suka buƙaci ya sauya matsaya kan harin.

    Ya ce ba a sanar da shi za a cimma wata yarjejeniya da Amurka za ta amince da ita ba inda ya ƙara da cewa Iran ba za ta mallaki makamin nukiliya ba.

    Sai dai ya gargaɗi cewa Amurka za ta zama a shirye ta kai gagarumin hari kan Iran idan har ba a cimma wata yarjejeniya ba.

    Wani babban kwamandan soji a Iran ya shaida wa Amurka cewa da ta guji sake yin kuskure.

    A ranar 28 ga Fabarairu ne sojojin Isra'ila da Amurka suka ƙaddamar da hare-hare ta sama ikan Iran yayin da Iran ɗin ta mayar da martani ta hanyar harba jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami kan wasu cibiyoyin Isra'ila da Amurka a sassan Yankin Gulf.

  4. Ukraine ta ƙaddamar da harin jirage mara matuƙa kan Rasha

    ...

    Asalin hoton, EPA/Shutterstock

    Yankuna da dama na ƙasar Rasha sun ce sun fuskanci hare haren jiragen sama marasa matuƙa na Ukraine.

    Magajin garin Moscow ya ce sun yi nasarar kakkaɓo huɗu daga irin waɗannan jirage da aka hari babban birnin da su.

    Can a yankin Yaroslavl na arewa maso gabas, gwamnan yankin ya sanar da hare haren jiragen da ya bayyana na abokan gaba - Ukraine.

    Ya ce an kai ga dakatar da motoci da sauran ababan hawa a kan titin da ya nufi Moscow, sannan kuma ya buƙaci jama'a da su guji bin wannan hanya.

    Can ma a yankin kudu maso yamma, a kusa da iyaka da Ukraine, gwamnan Rostov ya ce sun kakkaɓe hare-haren jiragen marasa matuƙa.

  5. WHO ta nuna damuwa kan bazuwar cutar Ebola a Congo

    ...

    Asalin hoton, Jospin Mwisha / AFP via Getty Images

    Hukumar lafiya ta duniya, WHO, ta ce a duk lokacin da ta faɗaɗa bincikenta a kan ɓarkewar cutar Ebola a gabashin jamhuriyar Dumukuradiyyar Congo, sai ta gano shedar cewa lalle cutar ta bazu.

    Wakilin BBC ya ce, wani kuma abin damuwa shi ne, a yanzu ta bazu zuwa yankin da ke da yawan jama'a sosai.

    Hukumomin ƙasar ta Kongo sun ce a yanzu mutanen da cutar ta hallaka sun kai sama da 130 - kuma ana samun ƙaruwar mutanen da suka kamu da cutar.

    To amma kuma gwamnatin ƙasar ta ce akwai jami'ai da ke aiki ba dare ba rana domin gano waɗanda ake ganin sun kamu ko sun yi mu'amala da waɗanda suka kamu.

    Hukumar ta lafiya ta buƙaci jama'a da kada su firgita.

    WHO, ɗin ta ce tana ƙoƙarin ganin ta daƙile bazuwar cutar ne ta hanyar taƙaita zirga-zirgar jama'a, da kuma faɗakar da mutane kan janaizar waɗanda suka rasu, ta hanyar da ta dace don gudun yaɗa cutar.

  6. Matasa sun harbe mutum uku a harin masallaci a San Diego

    ..

    Asalin hoton, EPA

    Wasu matasa biyu sun harbe mutum uku maza a wani masallaci da ke San Diego a California ta Amurka a wani hari da ake zargi na nuna ƙiyayya ne, kafin daga bisani su ɗauki rayuwarsu, kamar yadda ƴansanda suka bayyana.

    Lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Litinin, sa'oi biyu bayan da mahaifiyar ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi ta kira ƴansanda don shaida musu cewa ɗanta ya gudu tare da wani abokinsa kuma da alamu yana tunanin kashe kansa.

    Ƴansanda sun bazama neman matasan biyu lokacin da harin na San Diego ya soma inda suka samu mutum uku da raunuka sanadin harbin bindiga a wajen ginin.

    Jim kaɗan bayan nan sun sake samun wani kiran wayar cewa an ji ƙarar harbin bindiga daga wata mota. Ƴansan sun gano waɗanda ake zargi a mace - masu shekara 17 da 18 cikin wata mota nesa da masallacin.

    Daga cikin matasan akwai wani mai samar da tsaro da ke aiki a masallacin kuma ya taka muhimmiyar rawa wajen kare harin daga munanana, kamar yadda jami'ai suka ce.

    Hukumomi zuwa yanzu ba su tabbatar da sunayen mutanen ba sai dai mai samar da tsaro a masallacin mahaifi ne ga yara takwas, in ji wani da ya san shi wanda ya faɗa wa CBS.

  7. Maraba

    Masu bibiyar wannan shafi na Kai Tsaye, barka da warhaka. Da fatan mun wayi gari cikin ƙoshin lafiya.

    Kamar kullum, za mu ci gaba da kawo maku labarai kan yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Kuna kuma iya zuwa shafukanmu na sada zumunta domin kallon bidiyo da tafka muhawara kan labaran da muka wallafa.