Majalisar dokokin Zimbabwe ta amince da ƙudirin tsawaita wa'adin mulkin shugaban ƙasa

Asalin hoton, EPA
Majalisar dokokin Zimbabwe ta amince da ƙudirin tsawaita wa'adin shugaban ƙasa daga shekara biyar zuwa bakwai, wanda zai bai wa shugaba Emmerson Mnangagwa damar ci gaba da yin mulki har zuwa shekara ta 2030.
Fiye da yan majalisa 200 ne suka kad a ƙuri’ar amincewa da daftarin dokar a ranar Alhamis, wanda ya zarce matakin da ake buƙata na samun kashi biyu bisa uku domin yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin ƙasar.
Ƙudirin ya kuma soke batun gudanar da zaɓen shugaban ƙasa kai tsaye, inda daga yanzu ƴan majalisa ne za su riƙa zaɓen shugabannin ƙasar.
Mnangagwa, mai shekara 83, ya karɓi mulki ne a shekarar 2017 bayan hamɓarar da tsohon shugaban ƙasar Robert Mugabe tare da goyon bayan sojoji - kuma ya ci zaɓe a 2018 da 2023 da ake takaddama a kai.
A yanzu ƙudirin ya nufi majalisar dattiawa, inda kuma ake sa ran za a amince da shi kafin shugaban ƙasa ya zartar da shi a matasyin doka.





















