Mutum 65 sun mutu bayan ɓarkewar cutar Ebola a Congo

Asalin hoton, Universal Images Group via Getty Images
An tabbatar da ɓarkewar cutar Ebola a Lardin Ituri na Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo inda hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta Afirka ta ce an samu rahoton mutum 246 da ake zargin sun kamu, wasu 65 kuma sun mutu, galibi a Mongwalu da Rwampara.
Duka garuruwan sun dogara ne kan zinare a matsayin kafar samun kuɗaɗen shigarsu.
Gwaje-gwajen da aka yi a Kinshasa su gano mutum 13 cikin 20 ɗauke da ƙwayar cutar sannan kuma ana ci gaba da nazarin waɗanda ake zargin suna ɗauke da cutar.
Mutane huɗu da suka mutu na cikin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar.
Har yanzu gwamnatin ƙasar ba ta ayyana ɓullar cutar a matsayin ɓarkewa ba sai dai ana sa ran hukumomi su yi taron manema labarai nan gaba.


