Sudan ta mayar da jakadanta na Habasha gida
Sudan ta sanar da mayar da jakadanta gida daga Habasha bayan zargin makwabciyar tata da kuma Hadaddiyar Daular Larabawa da taimakawa wajen kai harin jirgin sama mara matuki, a filin jirgin saman Khartoum, babban birnin ƙasar.
Wakiliyar BBC ta ce harin na baya-bayan-nan ya haifar da fargaba a zuƙatan mazauna babban birnin, tare da ta'azzara rashin jituwa tsakaninta da Habasha.
Gwamnatin sojin Sudan ta ce tana da ƙwararan hujjoji da ke nuna cewa, dakarun RSF ne suka kaddamar da harin ta hanyar amfani da sararin samaniyar Habasha.
Sai dai Habasha ta yi watsi da zargin, inda ta bayyana shi a matsayin wani sabon zargi maras tushe, tare da zargin Sudan da bai wa mayaƙan da ke adawa da ita makamai.