China ta yi kiran a sake buɗe Mashigar Hormuz cikin gaggawa

Asalin hoton, TASNIM
Ministan harkokin wajen China Wang Yi ya yi kiran da a buɗe Mashigar Hormuz ''ba tare da ɓata lokaci ba'' a yayin da yake tattunawa da takwaransa na Iran.
Ministocin sun gana ne a Beijing a yau Laraba, a ziyarar Ministan harkokin wajen Iran Abba Araqchi na farko zuwa China tun bayan soma yaƙin.
Wang Yi ya kuma shaidawa Araqchi cewa cimma tsagaita wuta mai ɗorewa abu ne mai ''matuƙar muhimmanci'', inda ya ce akwai buƙatar a ci gaba da tattaunawa.
Ya kuma ce a shirye Beijing take ta taimaka wajen shawo kan lamarin.
Ganawar na zuwa ne mako guda kafin wata ganawa ta daban da Shugaba Trump ya tsara yi da shugaban China Xi Jingping, wanda ake hasashen shugabannin biyu za su tattauna kan yaƙin Iran da sake buɗe Mashigar.









