Yadda zan dawo da tallafin man fetur - Atiku
Yadda zan dawo da tallafin man fetur - Atiku
An wallafa
Kusan mako biyu ke nan ana ta ce-ce-ku-ce tun bayan da tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana aniyarsa ta cire tallafin man fetur idan ya hau kan mulki a 2027.
Kamar mutane da dama a Najeriya, Atiku na ganin cewa cire tallafin man fetur shi ne silar matsalolin matsin tattalin arziƙi da al'ummar ƙasar ke ciki.
"Ana cikin ƙunci, ana cikin rashi da rashin aikin yi, wannan tallafin man fetur da aka janye shi ne babban abin da ya haifar da hakan. Ban taɓa ganin an sha wahala ba a ƙasar nan kamar wannan lokaci," in ji Atiku a tattaunawar da BBC.



