KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 18/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 18ga watan Yulin 2026

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammad

  1. Sojojin Najeriya sun ce sun kashe 'ƴan ta'adda biyu da ceto mutum uku a Benue

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Whirl Stroke tare da haɗin gwiwar jami'an tsaron al'umma na jihar Benue sun kashe wasu da ake zargin 'yan ta'adda biyu tare da ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a wani samame da suka kai a ƙaramar hukumar Katsina-Ala ta jihar Benue.

    A cewar sanarwar rundunar, an fara aikin ne da misalin ƙarfe 3 na safiyar ranar 16 ga Yulin 2026, inda sojojin suka bi ta Takum a jihar Taraba zuwa ƙauyukan Tse Togo da Utenge da ke kusa da sansanin Orter, inda aka ce waɗanda ake zargin 'yan ta'addan ne ke fakewa.

    "A yayin musayar wuta kuma sojojin suka samu nasarar kashe mutum biyu daga cikinsu." in ji sanarwar.

    Mutanen da aka ceto dukkaninsu mazauna ƙaramar hukumar Katsina-Ala ne in ji sanarwar.

    Rundunar ta ce wasu daga cikin mutanen da aka yi garkuwa da su sun tsere daga sansanin yayin artabun.

    Sojojin sun kuma ƙwato makamai da harsasai daban-daban da kayan soji yayin samamen.

  2. Kotu ta yi watsi da ƙarar PDP ɓangaren Turaki

    ....

    Asalin hoton, @kabiruturakisan

    Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da ƙarar da wasu shugabannin jam'iyyar PDP suka shigar domin tilasta wa hukumar zaɓe ta INEC, ta amince da kwamitin riƙon ƙwarya na jam'iyyar ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki.

    Alƙali Salim Ibrahim ya yanke hukuncin cewa masu shigar da ƙarar ba su da hurumin gabatar da ƙarar. Saboda haka kotun ta ce ba ta da ikon sauraron shari'ar.

    Alƙalin ya ce masu ƙarar sun kasa tabbatar wa kotu cewa INEC ta taɓa amincewa da kwamitin riƙon ƙwaryar da suke goyon baya, ko kuma cewa suna da ikon shigar da ƙara a madadin jam'iyyar PDP.

    Shugaban kwamitin amintattu na PDP tsagin Turaki ƙarƙashin Sanata Adolphus Wabara, tare da wasu mambobin kwamitin ne suka garzaya kotu suna neman a umarci INEC ta sabunta bayananta tare da amincewa da kwamitin riƙon ƙwarya na jam'iyyar ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki.

    Sun kuma buƙaci kotun ta umarci hukumar zaɓen ta wallafa sunayen shugabannin riƙon ƙwaryar a shafinta na intanet.

    Sai dai wani tsagin jam'iyyar ƙarƙashin jagorancin Abdulrahman Mohammed da ke samun goyon bayan ministan birnin tarayya, Nyesom Wike, ya nemi shiga shari'ar tare da ƙalubalantar ikon kotun, inda ya ce shi ne shugabancin PDP halastacce, kuma masu ƙarar ba su da hurumin shigar da ita a madadin jam'iyyar.

  3. Me ya bambanta ƴansandan jihohi da 'askarawan' da gwamnoni suka samar?

    ....

    Asalin hoton, Zamfara state govt

    Ana ci gaba da tattaunawa a Najeriya kan shirin kafa rundunar ƴansandan jihohi, bayan Majalisar Dokokin tarayyar kasar ta amince da ƙudurin dokar.

    Majalisar ta amince da ƙudurin ne bayan karatu na biyu, inda aka zaɓi amfani da ƙudurin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar a maimakon wanda ƴan majalisa suka gabatar tun da farko.

    Buƙatar kafa ƴansandan jihohi dai ta daɗe tana cikin abubuwan da gwamnonin ƙasar ke nema. Sun yi ta jaddada cewa rashin ikon kafa rundunar ƴansanda ta jiha na hana su ɗaukar matakan da suka dace wajen magance matsalolin tsaro da ke addabar yankunansu.

    Tun kafin wannan yunƙuri, jihohi da dama sun riga sun kafa rundunonin tsaro na cikin gida, kamar ƴan sa-kai, ƴan banga da kuma askarawa, domin taimakawa jami'an tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyi.

    Sai dai akwai masu nuna damuwa cewa idan aka kafa ƴansandan jihohi, za su iya kasancewa tamkar waɗannan rundunonin da ake da su yanzu, waɗanda ake yawan zargin su da rashin ƙwarewa da kuma cin zarafin jama'a a wasu lokuta.

  4. Iran ta ce ta kai hari kan wuraren adana man Amurka a Bahrain

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Sojojin Iran sun yi iƙirarin cewa sun kai hari kan wuraren ajiyar jiragen sama da tankunan adana man fetur a sansanin Sheikh Issa da ke Bahrain, wanda suka bayyana a matsayin sansanin Amurka, ta hanyar amfani da jiragen yaƙi marasa matuƙa.

    A cikin sanarwar, sojojin sun kuma ce sun kai hare-hare kan gadoji da dama a Bahrain.

    Sai dai kawo yanzu, hukumomin Bahrain ko na Amurka ba su fitar da wata sanarwa ba game da girman ɓarnar da aka yi, ko kuma ko akwai waɗanda suka jikkata ko suka mutu sakamakon hare-haren.

  5. Hare-haren Amurka kan kayayyakin more rayuwar Iraniyawa laifin yaƙi ne - Iran

    Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya, Amir Saeed Iravani, ya aika wa Kwamitin Tsaro na MDD wasika inda ya yi kakkausar suka kan hare-haren da Amurka ta kai kan kayayyakin more rayuwar fararen hula a Iran.

    Iravani ya ce hare-hare da ake ci gaba da kai wa wuraren fararen hula, musamman muhimman hanyoyin mota da na jirgin kasa, sun saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa kuma sun kai matsayin laifin yaƙi.

    Jakadan ya kuma yi gargadin cewa idan Majalisar Dinkin Duniya da Kwamitin Tsaro ba su dauki matakin da ya dace ba, Iran za ta ci gaba da amfani da haƙƙinta da dokokin kasa da kasa suka tanada domin kare ikon ƙasarta, mutuncin yankinta, al'ummarta da muhimman muradunta na kasa.

  6. Assalamu alaikum

    Mabiya shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar, hutun ƙarshen mako.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.