NLC ta caccaki gwamnati kan taɓarɓarewar tsaro da tattalin arziki

Asalin hoton, Nigeria Labour Congress HQ/FB
Ƙungiyar ƙwadago a Najeriya ta soki yadda ake samun taɓarɓarewar matsalar tsaro da tattalin arziki a ƙasar.
A saƙon barka da sallah da Shugaban NLC, Joe Ajaero, ƙungiyar ta ce ma'aikatan Najeriya da talakawa na cikin ƙunci ƙarƙashin manufofin
A cewar shi, miliyoyin mutane na jurewa yanayin tsadar rayuwa da ke ƙara jefa mutane cikin talauci inda kuma ya yi kira ga ƴansiyasa da su yi nazari kan tasirin matakansu na tattalin arziki.
Mambobin NLC sun yi kira da a ɗauki matakai domin magance matsalar tsaro da ke ta'azzara a ƙasar.
Ajaero ya kuma ce ya kamata gwamnatoci su mayar da hankali wajen kare rayukan al'umma da kuma samar musu da abubuwan buƙata kamar abinci da kiwon lafiya da ilimi da kuma ayyukan yi.


















