Ba a mika mana wani shawarar shirin yarjejeniyar dena kai hari ba - Iran
Iran ta musanta rahotannin da ke cewa Saudiyya ta gabatar da shawarar rattaɓa hannu kan yarjejeniyar dena kai hari tsakaninta da wasu ƙasashen yankin.
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce a yayin da aka tambaye shi kan batun: “Ba zan iya cewa an gabatar da wani takamaiman shiri ba.”
A ‘yan kwanakin nan, wasu rahotanni da suka haɗa da na jaridar Amurka The Wall Street Journal sun bayyana cewa Saudiyya ta gabatar da shawarar ƙulla yarjejeniyar dena kai hari tsakanin Iran da ƙasashen yankin Gabas ta tsakiya ba..
A cikin rikicin da ya haɗa Iran da Isra'ila da Amurka wanda ya fara a ranar 28 ga Fabrairu, Iran ta ce ta kai hare-hare da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙi kan wasu wurare a ƙasashen yankin.