Duk wanda ke da hannu a harin Amurka kan tsibirin Larak zai ɗanɗana kuɗarsa - Iran

Asalin hoton, IRNA
Iran ta yi gargaɗin cewa duk wata ƙasa ko ɓangaren da ya taimaka wajen kitsa ko ya goyi baya ko ya shiga cikin shirin harin da Amurka ta kai tsibirin Larak zai ɗanɗana kuɗarsa kuma za su ɗauki alhakin sakamakon da zai biyo baya.
Iran ta ƙara da cewa za su kuma fuskanci martani mai tsanani kan abin da suka aikata.
A wata wasiƙa da jakadan Iran a Majalisar Ɗinkin Duniya ya aike wa Sakatare Janar na MDD da Kwamitin Sulhu, ƙasar ta yi Allah wadai da harin tare da kira ga Amurka da ta daina abin da ta kira take haƙƙin ƙundin tsarin MDD da kuma matakan da ke barazana ga zirga-zirgar jiragen ruwa a Tekun Fasha da mashigar Hormuz.
Haka kuma, rundunar sojin Iran ta yi gargaɗin cewa za ta mayar da martani kan duk wata ƙasa da aka yi amfani da yankinta wajen kai hare-hare kan Iran.















