An kama ɗan ƙasar Thailand a Afirka ta Kudu yana ƙoƙarin safarar ƙwai aku 50

Asalin hoton, Getty Images
An kama wani ɗan ƙasar Thailand a Afirka ta Kudu, yana ƙoƙarin safarar ƙwai 50 da ake zargin na wani nau'in aku ne da ke fuskantar barazanar bacewa, ta filin jirgin saman Johannesburg.
Ma'aikatar Muhalli ta Afirka ta Kudu ta ce jami'an kwastam sun gano ƙwayayen a ɓoye cikin wata jaka da aka ƙera a matsayin na'urar dumama ƙwai, wadda mutumin ke ɗauke da ita a matsayin jakar hannu a cikin jirgi.
Kamen ya biyo bayan wani makamancinsa da ya faru a filin jirgin a watan da ya gabata, lokacin da aka kama wani ɗan ƙasar Thailand ɗin da sama da ƙwai 400 na aku.































