Zaɓen gwamnan jihar Osun da abubuwan da ke wakana a Najeriya da sassan duniya 15/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo yadda zaɓen gwamnan Osun da sauran abubuwa ke wakana a Najeriya da sassan duniya 15/08/2026

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Aƙalla mutum 47 sun rasu sakamakon girgizar ƙasa a Indonesia

    Indonesia

    Asalin hoton, Getty Images

    Kawo yanzu mai'akatan ceto a Indonesiya ba su isa yankin da ya yi kusa da wurin da girgizar ƙasa ta yi kamari ba wacce ta afakawa yankin da ke gabashin gabar tekun ƙasar da sanyin safiyar yau Asabar.

    Zaftarewar ƙasa ta katse hanyoyi da hanyoyin sadarwa a yankin Nagekeo. Aƙalla mutum 47 ne suka rasa rayukansu a tsibirin Flores sakamakon girgizar ƙasar mai ƙarfin maki 7.7, yayin da jami'an agajin gaggawa ke ci gaba da neman masu saura numfashi.

    Wakilin BBC ya ce Girgizar ƙasar ta tada mutane daga barcinsu a yankuna da dama na wannan tsibiri mai tsaunuka. Sa'o'i kaɗan bayan haka kuma, wata girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 6.9 ta faru a tsibirin Sumatra da ke yammacin ƙasar.

  2. Ɗan takarar gwamnan Osun a APC ya ce jama'a su kare ƙuri'arsu

    Bola Oyebamiji

    Asalin hoton, Bola Oyebamiji/X

    Ɗan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaɓen gwamnan Jihar Osun, Bola Oyebamiji, ya buƙaci magoya bayansa da su kare ƙuri’un da suka kada a rumfunan zabe.

    Ya ce: “Kada ku bari wani, ta kowace hanya ko bisa kowane dalili, ya sauya ra’ayin jama’a ko ya lalata zaɓen."

    Oyebamiji ya bayyana hakan ne bayan hukumar zaɓe ta fara tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar.

    Ya ƙara da cewa: “Mun yi nisa sosai da wannan tafiya, don haka kada mu bari a lalata ƙoƙarin da muka yi gaba ɗaya. Mu ci gaba da zaman lafiya, sanya ido sosai da kuma kasancewa masu ƙwarin gwiwa yayin da muke jiran sakamakon ƙarshe. Allah Ya sa a bar ra’ayin jama’a ya yi nasara.”

    Ɗan takarar na APC, wanda ya bayyana hakan a shafinsa na X, ya ce jama’a sun fito da yawa domin gudanar da zaɓen kamar yadda doka ta tanada.

  3. Ƴansanda sun kama ɗan majalisar jiha da 'ƴan daba sama da 100' a zaɓen Osun

    Osun

    Ƴan sanda a jihar Osun da ke kudancin Najeriya sun kama wani ɗan majalisar dokokin jiha tare da wasu mutane fiye da 100 da ake zargin 'yan daba ne na siyasa masu sanya abin rufe fuska, yayin da aka fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen gwamnan jihar da ake fafatawa mai zafi akansa.

    Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan ya ce an kama mutanen ne, waɗanda suka fito daga jihohin Ondo da Ekiti da ke makobtaka da jihar ta Osun , a gidan ɗan majalisar yayin wani samamen tsaro da aka gudanar a yau Asabar.

    Ya ce kamen wani ɓangare ne na ƙoƙarin da hukumomin tsaro ke yi na hana duk wata harkar da ka iya kawo cikas ga zaɓen ko kuma ta zubar da ƙimarsa da sahihancinsa.

    Matakin ya biyo bayan zargin da gwamnan jihar ya yi na cewa jami'an tsaro na taimaka wa wasu mutane masu sanya abin rufe fuska wajen hana gudanar da zaɓe cikin lumana a wasu yankuna.

  4. A ba ƴan Osun abin da suka zaɓa - Adeleke

    Ademola Adeleke

    Asalin hoton, Ademola Adeleke/X

    Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya yi kira ga hukumar INEC da ta tabbatar da bin doka da tsare-tsaren gudanar da zaɓe.

    Gwamnan ya bayyana hakan ne a shafinsa na X, a daidai lokacin da da aka fara tantancewa da ƙirga ƙuri’un da aka kaɗa a rumfunan zaɗe daban-daban a faɗin jihar, inda ya ce ya kamata “a bar jama'a su zaɓi wanda suke so."

    Ya yaba wa jami’an tsaro da aka jibge domin tabbatar da tsaron zaben, sannan ya bukace su da su ci gaba da sanya ido sosai yayin da tsarin zaben ke shiga matakin tattara sakamako, daga rumfunan zabe zuwa kananan hukumomi.

    Adeleke ya kuma bayyana cewa yana da kwarin gwiwa kan dukkan hukumomin da ke da hannu wajen gudanar da zaben, yana mai cewa gwamnatin tarayya ta yi kokari sosai wajen samar da tsaro a lokacin zaben.

    Ya ce, “Dimokuradiyya tana kasancewa mafi karfi ne idan muka mutunta zabin al’ummarmu tare da kare mutuncin kuri’unsu.”

    Adeleke ya kara da cewa: “Ga kowane dan jihar Osun, ina kira gare ku da ku ci gaba da zaman lafiya, bin doka da oda, tare da kasancewa masu kishin wannan lokaci na dimokuradiyya.”

  5. An ɗora sama da kashi 70 na sakamakon zaɓen Osun a shafin IRev

    Ademola Adeleke, Bola Oyebamiji, Najeem Salam

    Asalin hoton, Ademola Adeleke, Bola Oyebamiji, Najeem Salam/Facebook

    Fiye da kashi 50 cikin 100 na sakamakon zaɓen gwamnan Jihar Osun ne ya zuwa yanzu aka riga aka ɗora a na'urar tattara sakamako ta INEC ta IReV.

    Ya zuwa karfe 6:10 na yamma, lokacin da wakilinmu ya duba shafin, an gano cewa daga cikin rumfunan zaɓe 3,763 da ke jihar, an riga an ɗora sakamakon rumfunan zaɓe 2,183 a shafin, inda kowa zai iya shiga ya duba.

    Sai dai ko da BBC ta sake garzaya shafin da misalin ƙarfe 7:15 na yamma, ta ga an rubuta a shafin cewa an ɗora kashi 75.10 ne na sakamakon zaɓen

    IReV wata fasaha ce da hukumar INEC ta ɓullo da ita domin rage maguɗin zaɓe da rage kura-kuran da ka iya faruwa a lokacin zaɓe.

    Yadda tsarin yake shi ne, bayan baturen zaɓe ya tattara ƙuri’un da aka kaɗa a rumfa, sannan ya bayyana sakamakon ga mutanen da suke wurin, zai yi amfani da na’urar Biometric Voter Accreditation System (BVAS) wajen ɗaukar hoton fom ɗin da ake kira EC8A, wanda aka rubuta sakamakon ƙuri’un a kai, sannan ya aika da hoton kai tsaye zuwa shafin IReV.

    Wannan yana nufin cewa kowa zai iya shiga shafin ya duba ko kuma ya sauke sakamakon zaɓen a lokacin da yake shigowa daga rumfunan zaɓe daban-daban. Hakan kuma zai sa ya zama da wahala mutum ya sauya sakamakon da aka riga aka wallafa.

    Za a iya duba sakamakon zaɓen gwamnan Osun ɗin a nan.

    INEC

    Asalin hoton, Inec Irev

  6. Isra'ila ta kare harin da ya kashe mutum 11 ciki har da yara uku a Lebanon

    Netanyahu

    Asalin hoton, Reuters

    Isra’ila ta kare sabon harin da ta kai a kudancin Lebanon, wanda ya kashe mutum 11, ciki har da yara uku. Ofishin Firaministan Isra’ila ya ce an kai harin ne kan wani kwamandan Hezbollah, bayan da wasu sojojin Isra’ila uku suka jikkata a wani harin da aka kai cikin dare.

    Isra’ila ta kuma ce kwamandan ya yi amfani da iyalinsa a matsayin garkuwar dan Adam.

    Mai magana da yawun rundunar, Doron Spielman, ya ce hare-haren ya kamata su taimaka wajen fara tattaunawa mai ma’ana tsakanin bangarorin.

    Sai dai Hezbollah ta bukaci Lebanon ta dakatar da abin da ta kira tattaunawar wulakanci da Isra’ila, tana mai cewa za ta mayar da martani yadda ya dace.

    Shugaban Lebanon, Joseph Aoun, ya ce hare-haren sun aika da sako karara game da zagayen tattaunawar da za a yi na gaba.

  7. UAE ta zargi Iran da kai hari kan jirgin dakon man fetur dinta a mashigar Hormuz

    Hormuz

    Asalin hoton, Getty Images

    Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta zargi Iran da kai hari kan wani jirgin dakon man fetur dinta yayin da yake ratsa wa ta mashigar Hormuz a ranar Juma'a.

    Kamfanin Dillancin Labarai na UAE ya ce harin bai yi sanadin mutuwa ko jikkatar kowa ba, kuma an samu shawo kan lamarin.

    A wata sanarwa, ma'aikatar harkokin wajen UAE ta yi tir da kai hari kan jiragenta, tana zargin Iran da amfani da mashigar Hormuz wajen matsa lamba ga wasu kasashe.

    UAE ta kuma buƙaci Iran da ta dakatar da irin waɗannan hare-hare tare da yin kira da a buɗe mashigar Hormuz gaba daya ba tare da wani sharadi ba.

    Rahotanni sun ce wasu jiragen kamfanin man fetur na Abu Dhabi guda biyu sun fuskanci matsala a mashigar a daren Alhamis.

  8. Sojojin sun kashe 'ƴan ta'adda' tare da ƙwace abubuwan fashewa 180 a Zamfara

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation FANSAN YAMMA sun kashe wasu 'yan ta'adda tare da kwace makamai da kuma kama wani da ake zargin yana kai wa 'yan ta'adda kayan fashewa guda 180 a jihar Zamfara.

    A cewar wata sanarwa da rundunar ta fitar, dakarun sun yi arangama da 'yan ta'addan ne a yankin Garin Kaso da ke ƙaramar hukumar Birnin Magaji yayin wani samame da suka kai.

    An kashe biyu daga cikin 'yan ta'addan tare da kwace bindigogi biyu, alburusai da babura biyu.

    Sanarwar ta ƙara da cewa yayin da samamen ke ci gaba, wasu 'yan ta'addan sun yi ƙoƙarin yi wa sojojin kwanton bauna daga maɓoyarsu, amma dakarun sun samu nasarar daƙile harin tare da tilasta musu tserewa.

    Rahotanni daga al'ummomin yankin sun nuna cewa an kwashe gawarwaki da kuma waɗanda suka jikkata daga cikin 'yan ta'addan bayan artabun.

  9. Ba ma iya samun Sheikh Jingir don ba shi shawara - Sheikh Nuru Khalid

    ....

    Asalin hoton, Sheikh Nuru Khalid/Facebook

    Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Nuru Khalid, ya ce akwai lokutan da sukan kasa samun damar ganawa da shugaban ƙungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa'iqamatis Sunnah, Sheikh Sani Yahaya Jingir, domin ba shi shawara kan wasu batutuwa da suka shafi al'umma da harkokin addini.

    Malamin ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da BBC Hausa, inda ya yi magana kan alaƙar da ke tsakanin malaman addinin Musulunci da yadda suke mu'amala da juna duk da bambancin ra'ayi da ake samu a wasu lokuta.

    Sheikh Nuru Khalid ya ce a matsayinsu na malamai suna ganin wajibi ne su riƙa tattaunawa tare da ba juna shawarwari idan akwai wani abu da suka ga ya kamata a yi wa gyara ko a yi bayani a kai.

    Sai dai ya yi zargin cewa ba koyaushe suke samun damar isar da irin waɗannan shawarwarin ga Sheikh Jingir ba.

    Sai dai malamin ya jaddada muhimmancin haɗin kai da fahimtar juna tsakanin malaman addini domin ciyar da al'umma gaba da kuma gujewa rikice-rikicen da ka iya tasowa sakamakon sabanin fahimta. Ana iya kallon cikakkiyar tattaunawar a shafin BBC Hausa na Facebook.

  10. ASUU ta nemi gwamnati ta biya malaman jami'o'i albashin da aka riƙesu

    Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta ASUU ta sake buƙatar gwamnatin tarayya ta biya albashin da aka riƙe wa malamai tare da warware sauran matsalolin jin daɗin ma'aikatan jami'o'i.

    Shugaban ASUU, Farfesa Christopher Piwuna, ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai a Jami'ar Jos, inda ya ce gwamnati ta cika sauran sharuddan yarjejeniyar da ta ƙulla da ƙungiyar a watan Disamban 2025 domin dawo da zaman lafiya a jami'o'in gwamnati.

    Ya ce warware waɗannan matsaloli zai taimaka wajen ƙarfafa gwiwar malamai da ba su damar mayar da hankali kan koyarwa, bincike da hidimtawa al'umma.

    ASUU ta kuma yi kira ga gwamnati ta ba ilimi muhimmanci, ta inganta kuɗaɗen da ake warewa jami'o'i, da kuma samar da manufofin tattalin arziki da za su rage talauci da samar da ayyukan yi ga 'yan Najeriya.

  11. Iran ta ce matuƙan jiragen yaƙinta uku na hannun Qatar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani kwamandan rundunar sojin Iran ya ce matuƙan jiragen yaƙin ƙasar uku suna tsare a hannun Qatar, tare da kira ga Kwamitin Agaji na Duniya na Red Cross da ya taimaka wajen gano halin da suke ciki.

    Brigediya Janar Mohammad Bagherzadeh ya ce matuƙan sun shiga hannu ne bayan jiragen yaƙi kirar Su-24 guda biyu da suka tashi daga Shiraz domin kai hari wani sansanin soji a Qatar sun fuskanci harbi yayin dawowa, lamarin da ya tilasta musu ficewa daga jiragen.

    Ya bayyana sunayen matuƙan a matsayin Javad Salehi, Abdul Majid Dashtian da Imran Behroshian, yana mai cewa an kama su da ransu bayan aukuwar lamarin.

    Iran ta kuma zargi Qatar da hana matuƙan damar ganawa ko tuntuɓar iyalansu tsawon watanni shida duk da ƙoƙarin diflomasiyya da aka yi, yayin da ta ce hare-haren da matuƙan suka kai sun haddasa gagarumar ɓarna a wani sansanin Amurka da ke Qatar.

  12. Sojoji sun daƙile harin ISWAP a wani sansanin soji a Borno

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Hadin Kai sun yi nasarar daƙile wani harin da mayaƙan ISWAP suka kai sansanin sojin Fo (FOB) da ke Mandaragirau a ƙaramar hukumar Biu ta jihar Borno da sanyin safiyar Juma'a.

    A wata sanarwa, rundunar ta ce mayaƙan sun kai harin ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare ta hanyoyi biyu, amma tsarin sa ido da gargaɗi na sansanin ya gano motsinsu tun da wuri.

    Hakan ya bai wa sojoji damar tura dakaru da suka tare su, lamarin da ya janyo musayar wuta mai zafi.

    Sanarwar ta ƙara da cewa mayaƙan da suka yi ƙoƙarin kutsawa cikin sansanin ta wata hanya ta daban sun gamu da turjiya mai ƙarfi, wanda ya tilasta musu janyewa.

    Daga bisani sojojin sun bi sawunsu tare ƙwace makamai da sauran kayan aiki.

    Rundunar ta ce an kashe mayaƙan ƙungiyar da dama a harin inda ta kuma ce babu wani sojinta da ya mutu ko ya jikkata yayin artabun.

  13. Iran ta zargi Faransa da tsoma baki da kutse cikin harkokinta

    Ma'aikatar Leken Asirin Iran ta zargi gwamnatin Faransa da tsoma baki cikin harkokin cikin gida na ƙasar tare da yi mata kutse.

    A cikin wata sanarwa, ma'aikatar ta ce yayin gudanar da bincike kan wani zargin kutse daga ƙasashen waje, jami'ai sun gano wasu jami'an diflomasiyyar Faransa guda biyu a wani wurin taro na sirri da ake bincike a kai.

    Ta kuma zargi Faransa da ƙoƙarin kauce wa zarge-zargen ta hanyar yaɗa bayanai a kafafen watsa labarai.

    Iran ta ce bayan an gano jami'an diflomasiyyar, an mika su ga jakadan Faransa a Tehran ta hanyar da ta dace da dokokin diflomasiyya, tare da yin gargadin cewa za ta ɗauki mataki idan irin wannan shiga cikin harkokinta ya ci gaba.

    Sai dai tun a watan Yuli, ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noël Barrot ya zargi jami'an tsaron Iran da keta kariyar diflomasiyya bayan da aka tsare wasu ma'aikatan ofishin jakadancin Faransa na sa'o'i da dama domin yi musu tambayoyi.

  14. Masu zaɓe sun fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen gwamnan Osun

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu zaɓe a jihar Osun sun fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen gwamnan jihar da ke gudana a ranar Asabar domin zaɓar wanda zai jagoranci jihar na shekaru masu zuwa.

    Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Najeriya (INEC) ta fara tantance masu zaɓe da kuma kaɗa ƙuri'a da misalin ƙarfe 8:30 na safe, bayan kammala rarraba kayayyakin zaɓe zuwa rumfunan zaɓe a ƙananan hukumomi 30 na jihar.

    Jihar Osun na da waɗanda suka yi rijistar zaɓe kusan miliyan 2.3, kuma ana sa ran miliyan 1.9 daga cikinsu za su kaɗa ƙuri'a a zaɓen da ke gudana tsakanin 'yan takara 15.

    Gwamna Ademola Adeleke na cikin waɗanda suka kaɗa ƙuri'arsu da sassafe, yayin da ake ci gaba da gudanar da zaɓen a sassa daban-daban na jihar.

  15. 'Maganar Trump cewa mashigar Hormuz ta Amurka ce shaci-faɗi ce'

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Jaridar Wall Street Journal ta ruwaito cewa wani jami'in Fadar White House ya ce kalaman Donald Trump na cewa mashigar Hormuz ta Amurka ce shaci-faɗi ce, ba wata manufa ta hukuma ba.

    Trump ya bayyana a ranar Juma'a cewa mashigar Hormuz mallakin Amurka ce.

    Sai dai kalaman nasa sun jawo martani daga Iran, inda mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar, Kazem Gharibabadi, ya ce mashigar Hormuz "ta Iran ce, kuma zai ci gaba da kasancewa hakan.

  16. Mutum bakwai sun mutu a harin Isra'ila a kudancin Lebanon

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Mutum bakwai sun mutu yayin da wasu uku suka jikkata sakamakon wani hari da Isra'ila ta kai a kudancin Lebanon a safiyar Asabar, a cewar Kamfanin Dillancin Labaran Ƙasar.

    Rahotanni sun ce wani jirgin yaƙin Isra'ila ya kai hari wani gida da ke wajen ƙauyen Ansar, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutanen tare da rusa gidan gaba ɗaya.

    An kuma ruwaito cewa sojojin Isra'ila sun tarwatsa wasu gidaje a garin Bint Jbeil da ke kusa da kan iyaka.

    Wannan shi ne mafi yawan mutanen da suka mutu a hari guda tun bayan yarjejeniyar watan Yuni da ta rage faɗace-faɗace tsakanin Isra'ila da Hezbollah.

    A gefe guda, babban sakataren Hezbollah, Naim Qassem, ya zargi jami'an Lebanon da matsa wa rundunar sojin ƙasar lamba ta hanyar aiwatar da yarjejeniyar da ta haɗa da kwance ɗamarar Hezbollah da tura sojojin Lebanon zuwa kudancin ƙasar.

  17. An kai hari kan wani jirgin dakon kaya a mashigar Hormuz

    Hukumar Kula da Harkokin Kasuwancin Ruwa ta Birtaniya (UKMTO) ta ce an kai wani hari da ba a san wanda ya kai shi ba kan wani jirgin dakon kaya a mashigar Hormuz, wanda ya yi sanadin lalacewa a jikin jirgin.

    A cewar rahoton, dukkan ma’aikatan jirgin na cikin ƙoshin lafiya, kuma babu wanda ya jikkata.

    Har yanzu ba a bayyana girman ɓarnar da harin ya yi wa jirgin ba, yayin da kuma ba a san irin tasirin da lamarin zai yi ga muhalli ba..

  18. Harin Iran ya illata tsarin sufurin babban jirgin ruwan yaƙin Amurka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Harin makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi da Iran ta kai sansanin sojojin ruwan Amurka da ke Bahrain ya illata tsarin samar da kayayyaki ga jirgin ruwan yaƙi na USS Abraham Lincoln da sauran jiragen Amurka a yankin, in ji New York Times.

    Jaridar ta ce harin ya lalata wani muhimmin wuri na samar da kayan aiki da rundunar sojojin ruwan Amurka ke amfani da shi, lamarin da ya tilasta Pentagon ƙara dogaro da sansanin Diego Garcia mai nisa domin tallafa wa ayyukan jiragen ruwanta.

    Rahoton ya ƙara da cewa hakan ya haifar da ƙarancin wasu kayayyaki da kuma ƙarin nauyi kan ma'aikatan jiragen ruwan da ke aiki a yankin.

    USS Abraham Lincoln ya shafe kusan watanni tara yana wannan aiki, kuma ana sa ran USS George Washington zai maye gurbinsa nan gaba.

  19. Iran ta ce har yanzu ba ta yanke shawarar komawa tattaunawa da Amurka ba

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya ce har yanzu ƙasarsa ba ta yanke wata shawara kan komawa tattaunawa da Amurka ba, yana mai jaddada cewa tattaunawar da ya yi da Qatar da Pakistan “ba ta nufin an fara shawarwari.”

    A lokaci guda kuma, shugaban Amurka Donald Trump ya yi iƙirarin cewa bayan abin da ya kira “shan kashin da Iran ta yi”, zai ayyana mashigar Hormuz a matsayin mallakin Amurka, sai dai Tehran ta musanta batun.

    Jaridar Wall Street Journal ta ruwaito wani jami’in Fadar White House na cewa kalaman Trump wasa ne kawai.

    Trump ya kuma yi magana kan abin da ya kira “mummunar barazanar tattalin arziƙin Iran, yayin da shugaban ƙasar Masoud Pezeshkian ya yi gargaɗin raguwar kuɗaɗen shiga daga man fetur da kuma sabon hauhawar farashin kayayyaki a ƙasar.

  20. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,barkanmu da wannan safiya ta ranar Asabar..

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarn abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.