Ba na son ƙulla wata yarjejeniya da Iran - Trump

Asalin hoton, Getty Images
Shugaban Amurka Donald Trump ya musanta wani rahoto da ABC News ta wallafa a daren Talata, inda ya zargi kafar da ya ƙirƙirar labaran ƙarya da bayar da rahoton cewa gwamnatinsa na ƙoƙarin tilasta Iran ta shiga tattaunawa.
Trump ya ce ba shi da sha’awar ƙulla wata yarjejeniya da Tehran.
"Saɓanin abin da ABC, wadda nake kira Fake News, ta ruwaito, ba na ƙoƙarin dawo da Iran kan teburin tattaunawa. Ba ni da wata sha’awa ga su sa hannu kan wata yarjejeniya da ba ta da wani amfani a gare su," in ji Trump kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Truth Social.
"Na fi son halin da ake ciki a yanzu, inda muke daf da samun cikakken iko kan mashigin Hormuz, yayin da tattalin arzikin Iran ke ci gaba da durƙushewa gaba ɗaya. Suna kawai ƙoƙarin jinkirta abin da babu makawa zai faru."
A ƙarshen saƙonsa, shugaban na Amurka ya ce "Yaushe mutanen Iran za su tashi su yi gwagwarmaya?"
Kalaman Trump sun zo ne sa’o’i kaɗan bayan da ya bayyana sabbin hare-haren da Amurka ta kai a kusa da mashigin Hormuz a matsayin "waɗanda suka dace", tare da gargadin cewa Washington za ta kaddamar da hare-hare masu ƙarfi fiye da haka idan Iran ta ɗauki matakin ramuwar gayya.
Iran ta ce hare-haren sun auka kan fararen hula da ke halartar wani bikin aure a ƙauyen Kohstak Sirik, inda aƙalla mutum biyar suka mutu, ciki har da yaro ɗaya.
Kafafen yaɗa labarai na Iran sun kuma ruwaito cewa mutane sama da 60 sun jikkata a harin.




















