Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Litinin 14/09/2026

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Hoto
  • Cyber Truck
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba da Usman Minjibir

  1. An kama wasu da ake zargi da kai hari jihar Oyo

    Gwamnatin Jihar Oyo ta tabbatar da cafke wasu mutum biyar da ake zargi da hannu a harin da ’yanbindiga suka kai kan sansanin dakarun hadin gwiwa na Operation Burst a Karamar Hukumar Oorelope, lamarin da ya haifar da zaman dar-dar a yankin Oke-Ogun.

    Mazauna yankin sun ce maharan dauke da muggan makamai ne suka mamaye sansanin sojojin ne da mislain karfe 5 na asuba zuwa 6 na safiyar Lahadi, tare da budewa jami'an tsaron da ke gadin sansanin.

    Sun kuma cinnawa wani bangare na wurin wuta da kona motar jami'an tsaro ta sintiri, sannan babu asarar rai ko jikkata ya yin harin.

    Wannan hari na zuwa kasa da sa’oi ashirin da hudu da Hukumar tsaro ta farin kaya DSS a kasar ta sanar da cewa wasu ‘yan ta’adda na shirin kafa sansani a Jihar Osun domin jin dadin kai hare-hare a shiyyar gabanin babban zabe na shekara ta 2027 a Naeriya.

    Maharan sun kuma yi awon gaba da injin bada wutar lantarki da Babur. Mukdashin gwamnan jihar Oyo Mista Bayo Lawan ya kai ziyarar gani da ido a inda aka kai harin.

  2. Matakai 4 da za ku bi domin sayen hannun jari

    A ranar Litinin ɗin nan ne matatar Ɗangote ta fara sayar da hannun jarin da ta ce za ta sayar ga al'ummar Najeriya domin bai wa duk wani ɗan ƙasar damar mallakar wani kaso a kamfanin.

    Ga matakan da za ku bi domin mallakar hannun jarin.

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon
  3. Trump na sukar masu masu kiran ayi ta ka tan-tsan kan AI

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ƙara tsananta sukar da yake yi kan kiraye-kirayen da wasu manyan shugabannin kamfanonin fasaha suka yi na a yi taka-tsantsan game da saurin ci gaban fasahar kirkirarriyar Basira ta AI.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Shugaba Trump ya bayyana ikirarin cewa ƙirƙirarriyar basirar ta AI za ta iya mamaye duniya ko kuma ta halaka bil'adama a matsayin yaudara.

    Trump ya ce ba za a dakatar da fasahar ba, tare da gargadin cewa dokokin da za a sanya mata na iya jefa kamfanonin fasahar cikin ƙunci matsin tattalin arziƙi.

    Ya kara da cewa ƙirƙirarriyar basira da cibiyoyin adana bayanai na iya zama manyan hanyoyin bunƙasa tattalin arzikin Amurka a tarihi. Ya kuma ce Amurka na buƙatar ci gaba da kasancewa kan gaba a fannin, domin kada China ta yi mata fintinkau.

    Hakan na zuwa ne bayan da jerin gargadin da wasu ma'aikatan masana'antar fasahar suka yi kan illolin da ƙirƙirarriyar basira mai ƙarfi za ta iya haifarwa. Jack Clark, na kamfanin Anthropic, ya shaida wa BBC cewa ya kamata kamfanonin AI su samar da wata hanyar rage tasirinsa, da kuma ɓangare da zai tabbatar da ingancinta.

    Ya kuma yi godiya Shugaba Trump kan yadda yake maida hankali kan wannan batu, amma ya yi gargadin cewa Amurka na iya rasa matsayinta na kan gaba a fannin AI idan jama'a suka daina amincewa da fasahar sakamakon wani mummunan haɗari ko bala'i.

  4. 'Arzikin Dangote ya haura dala biliyan 50 bayan fara sayar da hannayen jari'

    Dangote

    Asalin hoton, Getty Images

    Mujallar Forbes mai ƙididdigar attajiran duniya ta bayyana cewa arzikin attajirin na Najeriya, Aliko Dangote ya ƙaru da kusan dala biliyan 20, sakamakon fara sayar da hannayen jarin matatar mansa.

    Haka kuma akwai yiwuwar dukiyarsa ta sake ƙaruwa yayin da matatar man fetur tasa, mafi girma a Afirka, ke ci gaba da sayar da hannun jari ga ɗaiɗaikun masu zuba jari.

    Mutumin da ya fi kowa arziki a Afirka, Aliko Dangote, zai fara bai wa jama'a damar mallakar hannun jari a matatar man fetur ɗinsa da yake gudanarwa a matsayin kamfani mai zaman kansa, daga ranar Litinin 14 ga watan Satumba.

    Ana sa ran wannan sayar da hannun jari na farko ga jama'a (IPO) zai kasance mafi girma a tarihin nahiyar Afirka.

    Attajirin da ya yi fice a harkar siminti zai sayar da hannun jari har biliyan 4.1, wanda ya kai kashi 3.3 cikin 100 na kamfanin, kan farashin kimanin naira 525.

    Za a rufe karɓar buƙatun sayen hannun jarin a ranar 13 ga watan Oktoba, inda hannun jari 10 ne mafi ƙaranci da mutum zai iya saya.

    Ana sa ran za a fara cinikin hannun jarin a kasuwar hada-hadar hannayen jari ta Najeriya a watan Nuwamba.

    "Wannan rana ce mai matukar muhimmanci a garemu," in ji Dangote a wata hira da mujallar Forbes, yana mai bayyana cewa a ƙurarren lokaci ya samu tabbacin ranar da za a fara IPO ɗin, lamarin da ya sa ya makara zuwa wani taron masu zuba jari a ƙasar Canada, wanda tun da farko ya yi wa Firaministan ƙasar, Mark Carney, alƙawarin halarta.

    ''Dalilin da ya sa muke sayar da waɗannan hannayen jari yanzu shi ne domin tabbatar da cewa mun samar wa mutane ma damar samun arziki."

  5. EFCC ta gargaɗi lauyoyi kan cajin kuɗaɗen waje ga abokan hulɗa

    Hukumar yaki da yi wa tattalin arziki zagon ƙasa ta Najeriya EFCC, ta gargaɗi lauyoyin ƙasar su guji tilasta wa abokan hulɗarsu biyansu da kuɗaɗen ƙasar waje idan sun yi musu aiki, inda ta ce hakan ya zabawa doka.

    Wannan na ƙunshe cikin sanarwar da EFCC ta wallafa a shafinta na X a jiya Litinin, bayan kammala tattaunawa tsakanin su da wakilan kungiyar lauyoyi ta kasar NBA.

    Hukumar ta kuma yi gargadin duk lauya ko ma'aikacin fannin shari'a da aka samu da laifin, zai iya fuskantar shari'a.

    Muƙaddashin daraktan ofishin hukumar EFCC shiyyar Lagos Bawa Usman Kaltungo ya bayyana hakan ga shugaban ƙungiyar lauyoyin masu kula da aikata ayyukan da ba su dace ba, Moshood Abiola.

  6. Mayaƙan Houthi sun sake kai hare-hare kan cibiyoyin soji a Saudiyya

    Mayaƙan Houthi

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƴan tawayen Houthi na Yemen sun sake kai hare-hare kan cibiyoyin soja a Saudiyya ta amfani da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa a ranar Litinin.

    Houthi sun ce sun harba jirage marasa matuƙa da kuma makamai masu linzami da dama zuwa cikin ƙasar Saudiyya.

    Bayan hare-haren, hukumomin kare fararen hula na Saudiyya sun fitar da gajeren gargaɗi ga mazauna biranen Khamis Mushait da Abha, waɗanda ke kusa da iyakar Yemen.

    A baya-bayan nan ne Houthi suka ƙwace iko da gaɓar Tekun Maliya da kuma mashigar ruwan Bab al-Mandab.

    Muhimmancin wannan hanyar ruwa ya ƙaru sakamakon matsalolin da suka addabi zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz a lokacin yaƙin Amurka da Iran.

    Wani mazaunin birnin Khamis Mushait a Saudiyya ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa ya ji "manyan ƙarar fashe-fashe" waɗanda suka haddasa gobara da ta ci gaba da ƙonewa "na dogon lokaci".

    "Ko kaɗan ba mu samu damar yin barci ba," in ji shi.

  7. NDLEA ta kama muggan kwayoyin Colorado a Lagos

    Jami'an NDLEA

    Asalin hoton, NDLEA

    Bayanan hoto, Hukumar NDLEA na yawan kama muggan kwayoyi da hodar iblis da ake shiga da ita kaar

    Hukumar hana sha da fataucin muggan kwayoyi ta Najeriya NDLEA, ta sanar da kama wata nau'in tabbar wiwi da ake kira Colarado a filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Muhammad da ke birnin Lagos. Hukumar ta ce nauyin ta ya kai sama da sama da kilogram 27, da aka boye a cikin wani jirgin daukar kaya da ya fito daga kasar Birtaniya.

    Sun kuma kama wani da ake alakantawa da kayan mai suna Abidin Jide Salami, da ya zo daukar kayan a madadin dan uwansa da ke can Birtaniya, ta amfani da wata lambar sirri. NDLEA ta kuma kama kunshi biyu na Colorado da aka boye a cikin kayan kade-kade mai nauyin sama da kilogiram 44, a wata tashar mota a birnin Lagos din, sun kuma yi nasarar cafke akalla mutum 6 da ake zargi.

    Jami'in hulda da jama'a na hukumar NDLEA, Mista Femi Baba Femi, ya tabbatarwa da BBC kamen muggan kayan mayen da wadanda ake zargi.

  8. Rashin sufuri na baraza ga fannin lafiya a Gaza

    Marasa lafiya a sibitin Gaza

    Asalin hoton, Getty Images

    Jami'ai a birnin Gaza sun yi gargadin fannin lafiyar yankin na gab da rushewa, sakamakon dakatar da sufurin da jami'an lafiya ke amfani da su. Ma'aikatar lafiya a Gaza ta ce karancin man fetur, da man juye da kayayyakin gyaran mota na daga cikin dalilan da suke hana yawancin likitoci da malaman jinya gagara zuwa zuwa aiki asibiti.

    Ma'aikatan asibiti sun ce yawanci gidajensu na da nisa daga asibitocin da suke aiki, wadanda gidajensu ke kusa kuma yaki ya daidaita su dole suke zaune a wurare mai nisa.

    Tun bayan fara yaki tsakanin Hamas da Isra'ila a shekarar 2023, fannin lafiya a zirin Gaza ke cikin mawuyacin hali, sakamakon yawan wadanda hare-hare ke jikkatawa da rasa rayuka.

  9. Ku yi nazarin alƙawuran jam'iyyu kafin zaɓar dantakara - Sultan

    Sarkin Musulmai Muhammad Sa'ad

    Asalin hoton, Daular Usmaniyya

    Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya yi kira ga ƴan ƙasar su yi kyakkyawan nazari kan alƙawuran da ƴantakara suka yi musu, kafin su zaɓi wanda suke so ya wakilce su a babban zaɓen ƙasar da ke tafe na 2027.

    Sarkin Musulmi ya kuma gargaɗi ƴansiyasa kan matalar tsaro da sauran ƙalubalan da ake fama da su a gangamin yaƙin neman zaɓe, da kiran su mai da hankali kan batutuwan da za su wanzar da zaman lafiya da haɗin kai da cigaban ƙasa.

    Ya dai yi kalaman ne a lokacin da ya karɓi bakuncin kwamitin neman zaɓe na jam'iyyar APC mai mulki, ƙarƙashin jagorancin babban daraktan yaƙin neman zaɓen shugaba ƙasa, Sanata Abdul-Aziz Yari Abubakar, a fadarsa da ke Sakkwato.

    A ƙarshe Sarkin Musulmin ya yi wa kwamitin yaƙin neman zaɓen jam'iyyar APC fatan alkhairi, da addu'ar zaman lafiya da tsaro a ɗaukacin Najeriya.

  10. An kashe matafiya 9 a harin ƴanbindiga a Filato

    Jihar Filato

    Asalin hoton, ADO MUSA

    Bayanan hoto, Jihar Filato ta jima ta na fama da rikicin addini da kabilanci

    Rahotanni daga jihar Filato da ke arewa ta tsakiyar Najeriya na cewa mutum 15 sun rasu a hare-hare daban-daban da ƴanbindiga suka kai kudancin birnin Jos.

    A ranar Lahadi ne ƴanbindiga su ka kai hari yankunan Mangu da Riyom, lamarin ya rutsa da wasu matafiya.

    Tara daga cikin mutanen fasinjoji ne da ke kan hanyar zuwa birnin Jos, da ƴanbindigar suka buɗe musu wuta a ƙauyen Dungus.

    Sai kuma sauran 6 suka gamu da ajalinsu a Mangu da Riyom, kamar yadda shugaban ƙungiyar matasan Riyom, Barista Dalyop Solomon Montrey ya shaida wa BBC.

    ''Da daddare ƴanbindigar suka kai harin, a kan babbar hanyar zuwa Abuja idan an wuce garin Mararrabar Jama'a, sun fara kashe direban motar da wasu mutane amma daga baya adadin waɗanda suka rasu ya kai 9 a wurin. Akwai matanƙkabilar Birom da Hausawa da suka fito daga kasuwa akwai kuma yara. Ƴanbindigar sun kai hari ƙaramar hukumar Mangu sun kashe mutum 2, suka dangana da Riyom tare da hallaka mata biyu wanda ba ma ayi jana'izarsu ba.''

    Jihar Filato na fama da matsalar tsaro da rikice-rikicen addini da ƙabilanci, da ke janyo hasarar rayuka da dukiyar jama'a.

  11. Ghana ta cafke masu alaka da hodar iblis da aka kama a Faransa

    Hukumomi a kasar Ghana sun sanar da kama mutum uku da ake zargi, bayan cafke kusan tan 3.9 na hodar iblis da darajarsu ta kai sama da dala miliyan 260 a kasar Faransa, da aka boye cikin tarkacen robobi daga Ghana.

    Hukumar da ke sa ido kan fataucin muggan kwayoyi ta Ghana, ta ce wadanda ake zargin su ke kula da harkar a kasar a madadin wani mai suna Jos Leijdekkers, da aka fi sani da sunan ‘‘Bolle Jos'' da ke zaune a kasar waje.

    Hukumar ta ce ana gudanar da binciken mutanen domin sanin karin mutanen da suke safarar muggan kwayoyi a kasar. Leijdekkers na daya daga cikin dillalin hodar iblis da hukumomi a Turai ke nema ruwa a jallo, bayan yanke masa hukuncin zaman kason shekaru 24 alhalin baya kotun.

    An yi amanna ya na zaune a kasar Saliyo, ko da yake gwamnatin kasar ta ce ba ta da masaniya kan inda ya ke. A bangare guda kuma babbar jam'iyyar adawa a Ghana NPP, ta bukaci a gudanar da bincike mai zaman kan shi kan hodar iblis da aka kama a baya-bayan nan, inda suka ce wadda aka kama a kasar a shekarar da ta gabata ta kai darajar dala biliyan daya.

  12. Kungiyar OLA a Habasha ta gargadi kamfanonin hakar ma'adinai a Oromia

    Wata ƙungiya masu ɗauke da makami a yankin Oromia na ƙasar Habasha ta yi barazana ga kamfanonin haƙar ma'adinai da ke aiki a yankin, tare da fitar da sabbin jerin buƙatu da dole su cika idan suna son ci gaba da aikinsu.

    Kungiyar Oromo Liberation Army (OLA), wadda gwamnatin Addis Ababa ta ayyana a matsayin ƙungiyar ta'addanci tun kusan shekaru goma da suka gabata, tana son dukkan kamfanonin haƙar ma'adinai su riƙa ɗaukar ma'aikata daga yankunan da suke aiki.

    Sannan su bi ka'idojin kare muhalli domin tabbatar da ɗorewar ayyukan haƙar ma'adinai. Yankin Oromia shi ne mafi yawan al'umma a Habasha, kuma yana da manyan wuraren hakar ma'adanan zinari. Wannan wa'adin da ƙungiyar ta bayar na zuwa ne makonni kaɗan bayan da aka kashe mutane da dama a wani hari da aka kai a wani wurin haƙar ma'adinai a yammacin yankin.

  13. An yi jana'izar yara 26 a DR Congo

    An gudanar da jana'izar yaran da suka rasu a gobarar da ta faru a wata makaranta a yammacin Jamhuriyar Dimukradiyyar Congo a makon da ya wuce. Akalla yara 26 ne gobarar ta rutsa da su a ranar Alhamis din makon jiya, a lokacin da suke daukar karatu a Bukavu. Birnin dai na karkashin ikon 'yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda, kuma yawancin yaran sun gamu da ajalinsu yayin da suke kokawar fita daga ajin lokacin da gobarar ta tashi. Kawo yanzu ba a san abin da ya haddasa ta ba.

  14. An gargaɗi ƴan Zambiya kan cin mushen dabbobi sakamakon cutar anthrax

    Dabba

    Asalin hoton, Reuters

    Hukumomi a Zambiya sun gargaɗi ƴan ƙasar da su guji cin naman dabbobin daji bayan da dabbobi da dama suka mutu sakamakon cutar anthrax.

    Wani jami'i na hukumar kare afkuwar bala'i ya ce a ƙarshen makon da ya gabata, mutum 12 ne suka kamu da cutar bayan da suka ci naman dabbobin a yankin kogin Munyamadzi.

    Jami'in ya yi kira ga jama'a da su guji cin naman dabbobin da ba a tantance dalilin mutuwarsu ba.

    Zuwa yanzu jami'ai ba su tantance girman ɓarkewar cutar a baya-bayan nan ba inda ake ci gaba da sa ido da kuma gwaji a ɗakin gwaje-gwaje.

    A shekarar 2023, ƙasar ta yi fama da ɓarkewar cutar da ba a yi tunani ba, har ta kai mutum huɗu sun mutu sannan kuma ta bazu zuwa larduna tara cikin 10.

  15. Sojoji sun gano lita 10,000 na mai da aka 'tace ta haramtacciyar hanya' a Rivers

    Ɗanyen mai cikin jarkoki

    Asalin hoton, @NigerianNavy

    Bayanan hoto, Ɗanyen mai cikin jarkoki

    Rundunar sojin ruwa ta Najeriya ta ce ta bankaɗo wani wajen ajiyar albarkatun mai ɗauke da lita 10,000 na man da ake zargin an tace ta haramtacciyar hanya.

    Cikin wata sanarwa ta Daraktan Yada labarai na rundunar, Abiodun Folorunsho, an yi bankaɗar ce a samamen da dakaru suka kai a ranar Asabar don daƙile satar ɗanyen mai a yankin Eleme Express na jihar Rivers.

    Ana zargin an samo man ne daga wani waje nesa da yankin wanda kuma aka ajiye domin sayarwa mutane.

    Rundunar ta ce an gano man cikin jarkoki 400 wadda kowace jarka ke ɗauke da mai lita 25 a ciki sai dai kuma babu wata haramtacciyar matata da aka gano a wajen.

    A cewar rundunar, baya ga bankaɗar, dakaru sun yi nasarar tarwatsa wata muhimmiyar cibiya ta samar da mai ta ɓarauniyar hanya.

    Sanarwar ta ƙara da cewa jami'an ba su samu cafke kowa ba kasacewar masu hada-hada a cibiyar sun tsere a lokacin da sojoji suka yi dirar mikiya a wajen.

  16. Yadda za ku sayi hannun jari

    Kasuwar hannun jari

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Kasuwar hannun jari

    A ranar Litinin ɗin nan ne matatar Ɗangote ta fara sayar da hannun jarin da ta ce za ta sayar ga al'ummar Najeriya domin bai wa duk wani ɗan ƙasar damar mallakar wani kaso a kamfanin.

    Kamfanin wanda zai sayar da hannayen jari guda biliyan 4.1 a kan farashin naira 525 kowane hannu, za a rufe sayarwar ne a ranar 13 ga watan Oktoban 2026.

    Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya sanar da cewa matatar man fetur ɗin nasa za ta fara sayar da hannayen jari ga jama'a ta hanyar Initial Public Offering (IPO), inda aka tsara bai wa kowa damar mallakar kaso a cikin kamfanin ko da da ƙaramin jari ne.

    Wannan cigaba ne da ya buɗe sabuwar tattaunawa kan muhimmancin kasuwar hannun jari da kuma damar da take samarwa ga matasa masu son gina makoma mai ɗorewa.

    Hakan ya sa ƴan Najeriya ke yin tambayoyi dangane da hanyoyin da ya kamata su bi domin sayen hannun jari a duk lokacin da irin wannan dama ta bujuro musu ba ma lallai a matatar Ɗangote kaɗai ba.

    Da yake sharhi kan wannan dama, Dr Salihu Lukman, Mataimakin Farfesa a University of Hafr Al Batin da ke ƙasar Saudiyya, ya ce kasuwar hannun jari na daga cikin hanyoyin da suka fi tasiri wajen tara dukiya cikin tsari da kuma dogon lokaci.

    Ku latsa nan domin samun bayani kan hanyoyin da ake bi don sayen hannun jari da ma samun ƙarin bayani.

  17. Hatsarin mota ya halaka aƙalla mutum 21 a Afirka ta Kudu

    Wani hatsarin mota ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 21 a Lardin Western Cape da ke Afirka ta Kudu.

    Jami'ai sun ce mutane da dama sun ji rauni a hatsarin da ya afku kusa da garin Prince Albert mai nisan kusan kilomita 300 daga Cape Town.

    Hukumomin Lardin sun rufe babbar hanyar lamarin da ya janyo cunkoson ababen hawa.

  18. Saudiyya ce ta nemi a soke tattaunawar Oman - Iran

    Kakakin ma'aikatar harkokin Iran Esmail Baghaei ya ce an soke tattaunawar a aka tsara yi a Oman tsakanin Iran ɗin da wasu ƙasashen Gulf bisa buƙatar da Saudiyya ta nema.

    Wannan wata dama ce da aka bai wa Iran da Oman kuma ana sa rai cewa ƙasashen yankin za su ci moriya da kuma una godiya ga hakan, kamar yadda Baghaei ya shaida.

    Ministocin harkokin wajen Iran da Oman sun sanar da soke tattaunawar a daren jiya kuma zuwa yanzu ba a sanar da ranar da za a yi tattaunawar ba.

    Sanarwar soke taron dai ta sa farashin ɗanyen mai ya zarce dala 108 kan kowace ganga guda.

  19. Iran ta kakkaɓo jirgi mara matuƙi a Mashigar Hormuz

    Jirgin Ruwa

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar Juyin juya halin Iran ta ce ta harbo wani jirgi mara matuƙi a Mashigar Hormuz.

    Kamfanin dillancin labarai na IRIB ya ruwaito cewa dakarun IRGC ne suka kakkaɓo jirgin na MQ-1 a Mashigar ta Hormuz.

    Kakakin rundunar ya ce sabon makaman tsaron sararin samaniyar IRGC ne suka harbo jirgin ruwan tare da lalata shi.

    Zuwa yanzu IRGC ba ta yi ƙarin bayani game da batun ba.

  20. Boko Haram ta lalata aƙalla makarantu 5000 a Borno - Zulum

    Babagana Zulum

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Babagana Zulum

    Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce Boko Haram ta lalata gine-ginen makarantu aƙalla 5,000, lamarin da ya sa yara miliyan 2.2 ba sa zuwa makaranta a lokacin da rikicin ta'addanci ya yi ƙamari.

    Gwamna Zulum ya bayyana waɗannan alƙaluma ne a lokacin ƙaddamar da wasu ayyuka a Maiduguri, jiya Lahadi.

    Kakakin gwamnan, Malam Dauda Iliya, ya shaida wa BBC cewa gwamna Zulum ya duƙufa wajen ganin an shawo kan matsalar tsaron tare da inganta fannin ilimi ganin irin girman ɓarnar da Boko Haram ta yi wa ɓangaren.

    A cewar kakakin, gwamnan ya gina azuzuwa kusan 5000 da gina wasu makarantu 129 sannan kuma ana sa ran kammala wasu 140 daga nan zuwa ƙarshen mulkinsa.

    Ya ce akwai yara sama da miliyan ɗaya da dubu 800 da suke makaranta saɓanin lokacin da gwamna Zulum ya karɓi mulki inda a lokacin yara dubu 800 ne kaɗai suke zuwa makaranta.

    Gwamna Zulum ya bayyana cewa Boko Haram ta kashe malamai da jami'an kula da makarantu da dama musamman a lokacin da yaƙin ya yi ƙamari.

    Zulum ya ce gwamnatinsa ta ware dala miliyan 35 a tsakanin shekarar 2025 da 2026 don inganta ilimin pramare da sakandare.