KAI TSAYE, Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 02/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan yaƙin Iran da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 02/06/2026.

  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba da Haruna Kakangi

  1. Isra'ila da Hezbollah na gwabza ƙazamin faɗa a Lebanon

    ..

    Asalin hoton, Kawnat Haju / AFP via Getty Images

    An ci gaba da gwabza ƙazamin faɗa a kudancin Lebanon duk da sanarwar da shugaba Donald Trump ya yi cewa Isra'ila da Hezbollah sun amince su daina faɗa da juna.

    Rahotanni sun ce ɓangarorin biyu sun kai wa juna hare-hare.

    Firayim Ministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya tabbatar da yarjejeniyar, amma ya yi gargaɗin cewa za a ci gaba da kai hare-hare ta sama idan ƙungiyar Hezbollah ta ci gaba da kai farmaki kan Israila.

    Shugaba Trump ya ce ya tattauna da Netanyahu da wakilan Hezbollah kan shirin, bayan da Iran ta yi gargaɗin cewa matakin sojan da Isra'ila ta ɗauka a Lebanon barazana ce ga yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran a halin yanzu.

  2. Rasha ta kai farmakin da ya halaka mutum 13 a Ukraine

    ....

    Asalin hoton, AFP

    Aƙalla mutum 13 ne aka kashe a jerin hare-haren da Rasha ta kai wa wasu biranen Ukraine ta hanyar amfani da jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami.

    Magajin garin Kyiv, Vitali Klitschko ya ce an kashe mutane huɗu a babban birnin ƙasar, sannan an raunata fiye da hamsin, ciki har da yara da dama.

    Wakilin BBC ya ce magajin garin Kyiv ya kuma ce an kai wa wani asibiti hari, lamarin da ya sa wani ɓangare na ginin rugujewa.

    Hukumomin birnin Dnipro da ke gabashin ƙasar sun ce mutane tara ne suka mutu a hare-haren da aka kai a can.

    Tun farko shugaba Zelensky ya ce bayanan sirri sun nuna cewa Rasha na shirin kai wa ƙasarsa gagarumin farmaki.

  3. Barka da Safiya

    A yau ma shafin Kai Tsaye na BBC Hausa na yi muku maraba, da fatan mun wayi gari lafiya.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Nabeela Mukhtar Uba tare da abokin aiki Haruna Kakangi za mu kasance tare da ku.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin kallon bidiyo da ma tafka muhawara game da labaran da muka wallafa.