Isra'ila da Hezbollah na gwabza ƙazamin faɗa a Lebanon

Asalin hoton, Kawnat Haju / AFP via Getty Images
An ci gaba da gwabza ƙazamin faɗa a kudancin Lebanon duk da sanarwar da shugaba Donald Trump ya yi cewa Isra'ila da Hezbollah sun amince su daina faɗa da juna.
Rahotanni sun ce ɓangarorin biyu sun kai wa juna hare-hare.
Firayim Ministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya tabbatar da yarjejeniyar, amma ya yi gargaɗin cewa za a ci gaba da kai hare-hare ta sama idan ƙungiyar Hezbollah ta ci gaba da kai farmaki kan Israila.
Shugaba Trump ya ce ya tattauna da Netanyahu da wakilan Hezbollah kan shirin, bayan da Iran ta yi gargaɗin cewa matakin sojan da Isra'ila ta ɗauka a Lebanon barazana ce ga yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran a halin yanzu.













