Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 25/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Asabar 25 ga watan Yulin 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammad

  1. Muna ƙoƙarin ceto shugaban ƙaramar hukumar Bunguɗu - Sojojin Najeriya

    Rundunar Operation FANSAN YAMMA ta ce jami'anta na bibiya tare da yunƙurin ceto shugaban ƙaramar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara, Nura Umar Abdullahi, bayan wasu ƴan bindiga sun yi awon gaba da shi daga gidansa, sannan ta ƙara da cewa an ceto wasu daga cikin iyalansa.

    A cewar rundunar, maharan sun yi nasarar yin awon gaba da shugaban karamar hukumar bayan sun yi galaba a kan jami'an ƴansanda da masu sintiri da ke ba shi kariya.

    Sanarwar ta ce bayan sojoji sun ji harbe-harbe ne suka garzaya wurin tare da bin sawun maharan, inda suka yi musayar wuta.

    Rundunar ta ce matsin lambar da dakarunta suka yi ya sa maharan ne ya sa suka bar mutum biyar daga cikin iyalan shugaban ƙaramar hukumar, waɗanda suka haɗa da 'ya'yansa biyu da mahaifiyarsa da matarsa da wani ɗan'uwansa, kafin su tsere da shi cikin daji.

    Rundunar ta tabbatar da mutuwar jami'an tsaronsa uku, ciki har da ƴansanda biyu da dan sintiri guda daya. Haka kuma wani ɗan babu ruwan ya rasu, sannan wani Alhaji Bello Umar, ya ji raunuka.

    Rundunar ta ce ta ƙaddamar da aikin haɗin gwiwa tare da ƴansanda da DSS da ƴan sa-kai domin gano inda maharan suke tare da kuɓutar da shugaban ƙaramar hukumar cikin ƙoshin lafiya.

  2. Abin da ya janyo taƙaddama tsakanin Tinubu da Atiku

    Da alama za a daɗe ba a kawo ƙarshen taƙaddamar da ke tsakanin fadar shugaban Najeriya Bola Tinubu da tsohon mataimakin shugaban ƙasar kuma ɗan takarar shugabancin Najeriya a zaɓen 2027 na jam'iyyar ADC Atiku Abubakar ba, inda dukkan ɓangarorin ke zargin juna da aikata rashawa da manyan laifuka.

    Jayayya ta baya-bayan nan tsakanin ɓangarorin ta taso ne bayan da fadar shugaban Najeriya ta zargi tsohon mataimakin shugaban ƙasan da ƙoƙarin yin zagon ƙasa ga siyasar ƙasarsa ta hanyar ɗaukar masu taya shi neman shiga a wajen gwamnatin Amurka, tare da tayar da wasu batutuwa da a cewar ta, ''an riga an wuce zamanin su.''

  3. An kori ɗalibai biyu daga jami’ar gwamnati a Kogi bisa zargin yin luwadi

    Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Confluence (Confluence University of Science and Technology - CUSTECH), mallakin gwamnatin jihar Kogi da ke tsakiyar Najeriya, ta kori ɗalibai biyu bisa zargin aikata luwadi.

    Jami’ar ta ce amince da hukuncin ne bayan ta yi nazarin shawarwarin Kwamitin Ladabtar da Ɗalibai.

    A cikin wata sanarwa da jami’ar ta fitar ranar Juma’a, ta ce:

    “An kori ɗalibai biyu saboda shiga harkar luwadi, sannan an dakatar da wasu ɗalibai huɗu na tsawon zangon karatu daya saboda laifin faɗa a harabar jami’a.”

    Jami’ar ta ce an ɗauki waɗannan matakan ne kamar kundin dokokin dalibtaka na makarantar ya nuna.

    Mahukuntan jami’ar sun ce za su ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da ladabi da kuma samar da yanayi mai kyau na karatu.

    Sun ƙara da cewa ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar tsauraran matakan ladabtarwa kan duk wani ɗalibi da aka samu da laifin karya dokoki da ƙa’idojin jami’ar.

    Haka kuma jami’ar ta bukaci ɗalibai su san dokokinta sosai tare da gudanar da kansu yadda ya dace.

    Najeriya na cikin ƙasashen Afirka da har yanzu ke haramta alaƙar jinsi tsakanin masu jinsi ɗaya.

    A shekarar 2014 ne aka sanya wa dokar Haramta Auren Masu Jinsi Ɗaya (Same-Sex Marriage (Prohibition) Act) hannu, wadda ta tanadi daurin shekaru 14 ga duk wanda ya yi aure ko wata alaka ta jinsi iri ɗaya.

    Dokar ta kuma haramta nuna soyayya a bainar jama’a tsakanin masu jinsi ɗaya, inda ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara 10.

    Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam sun sha sukar wannan doka, suna cewa ta ƙara tsananta wariya, cin zarafin masu sha’awar aure ko alakar auren jinsi.

    Wani rahoto na Human Rights Watch ya ce dokar ta “halatta cin zarafin mutanen LGBT a hukumance, lamarin da ya ƙara muni kan halin da suke ciki.”

    Masu fafutukar kare haƙƙin ɗan Adam sun ce har yanzu ana ci gaba da samun rahotannin hare-hare, dukan jama’a da kuma yi wa mutanen LGBT baƙar fata domin karɓar kuɗi, suna masu cewa dokar ta samar da yanayin da irin waɗannan cin zarafe-zarafen ke faruwa ba tare da cikakken ɗaukar mataki ba.

    A faɗin Afirka kuwa, ƙasashe da dama sun ƙara tsaurara dokokinsu yaki da auren jinsi. Kasashe irin su Ghana da Uganda da Burkina Faso duk sun tanadi matakai masu tsauri kan masu harkar.

  4. Za mu ci gaba da kai hare-hare har sai maƙiyanmu sun miƙa wuya - Iran

    Sakataren Majalisar Tsaron Ƙasar Iran, Mohammad Baqir Zulqadr ya bayyana cewa ƙasarsa za ta ci gaba da kai hare-hare "cikin tsari da kuma kan takamaiman wurare" har sai abokan gabanta sun miƙa wuya gaba ɗaya.

    Ya yi wannan furuci ne a lokacin da babu wani sabon rahoto cikin sa'o'i 24 da suka gabata game da hare-haren da aka kai tsakanin Amurka da Iran ko kuma martanin da ɓangarorin suka mayar wa juna.

    Zulqadr ya kuma yi iƙirarin cewa duk lokacin da aka ga hayaƙi ya tashi a yankin, hakan na nufin an kai hari ne kan wata cibiyar soji, ta tsaro ko kuma ta kuɗi ta Amurka.

    An naɗa shi a matsayin sakataren majalisar ne bayan mutuwar magabacinsa, Ali Larijani, wanda hukumomin Iran suka ce ya mutu sakamakon hare-haren Isra'ila da Amurka.

  5. Majalisar Iran ta tura ƙudurori 12 kan mashigar Hormuz zuwa kwamitin tsaro

    Majalisar dokokin Iran ta tura ƙudurori 12 da suka shafi mashigar Hormuz da kuma dokokin yankunan ruwa zuwa Kwamitin tsaron ƙasar domin nazari.

    Kakakin majalisar, Abbas Goodarzi, ya ce ƙudurori tara sun shafi mashigar Hormuz, yayin da uku suka shafi gyaran dokar yankunan ruwa.

    Kamfanin dillancin labaran majalisar Iran Khaneh Mellat ya ruwaito cewa, ana kuma sa ran Kwamitin Tattalin Arziƙi na majalisar zai yi nazari kan batun, musamman dangane da kuɗaɗen shiga da za a iya samu daga yadda ake gudanar da harkokin mashigar Hormuz.

    Batun kakaba kuɗin wucewa ga tankokin dakon mai da ke bi ta mashigar Hormuz ya ƙara ɗaukar hankali a Iran bayan yaƙin da aka yi tsakanin Amurka da Isra'ila da Iran.

    A makon da ya gabata, kakakin majalisar Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, ya wallafa a shafinsa na X cewa, "Yanayin da ake ciki a mashigar Hormuz ba zai koma yadda yake kafin yaƙin ba."

  6. Kotu ba ta NDLEA damar rusa masana'antar ƙwayar Meth ta Ogun

    Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta amince wa Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta rusa wani ɓoyayyen masana'antar ƙera ƙwayar sinadarin methamphetamine, wani nau'in miyagun ƙwayoyi.

    Wurin da ake zargin ana sarrafa ƙwayoyin yana cikin ƙauyen Iloti da ke dajin Abidagba a ƙaramar hukumar Ijebu East ta Jihar Ogun.

    Mai shari’a Musa Kakaki ya ba da umarnin rushe wurin tare da lalata wasu sinadarai da aka ƙwato daga hannun wasu ‘yan ƙasar Mexico uku da kuma ‘yan Najeriya bakwai da ake tuhuma da gudanar da haramtacciyar masana’antar.

    Sai dai kotun ta hana lalata wasu sinadarai da ake taƙaddama a kansu bayan lauyoyin waɗanda ake zargin sun nuna adawa, suna mai cewa sinadaran na iya zama muhimman hujjoji a shari’ar.

    NDLEA ta bayyana cewa sinadaran da aka gano suna da haɗari ga lafiyar jama’a kuma darajarsu ta kai kusan naira biliyan 480.

    Bayan sauraron hujjojin ɓangarorin biyu, kotun ta amince da buƙatar rushe wurin amma ta ɗage shari’ar zuwa ranakun 26, 27 da 28 ga watan Oktoba domin ci gaba da sauraron shari’ar da kuma yanke hukunci kan wasu sinadaran da ake gardama a kansu.

  7. Mayaƙan Houthi sun ce sun kai hare-hare a Saudiyya

    Mayakan Houthi da ke Yemen sun ce sun kai hare-hare kan wasu wurare a birnin Jizan na Saudiyya, a matsayin martani ga hare-haren sama da Saudiyya ta kai kan birnin tashar ruwa na Hodeida a Yemen.

    A baya, Saudiyya ta yi gargaɗi ga mazauna Jizan da Yanbu, waɗanda dukkansu ke da muhimmanci ga masana'antar man fetur ta ƙasar, amma daga baya ta janye gargaɗin cikin gaggawa.

    Ya zuwa yanzu, Saudiyya ba ta bayar da rahoton wata asara ko ɓarna sakamakon harin ba. Sai dai akwai rahotannin da ba a tabbatar da su a hukumance ba da ke cewa an ji ƙarar fashe-fashe tare da tashin gobara a wasu sassan birnin Jizan.

    Tun da farko, Saudiyya ta ce hare-haren saman da ta kai kan Hodeida martani ne ga hare-haren da 'yan Houthi ke kai wa kan jiragen ruwa a Tekun Bahar Maliya.

  8. ICC ta tsige mai gabatar da ƙara da jagoranci bayar da sammacin kama Netanyahu

    Ƙasashen da ke mambobin Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) sun kaɗa kuri'ar amincewa da tsige babban mai gabatar da ƙara na kotun, Karim Khan.

    Ana zargin lauyan ɗan Birtaniya mai shekara 56 da dabi'ar da ba ta dace ba - a kan wata karamar ma'aikaciyar kotun - zargin da ya musanta.

    Wakiliyar BBC ta ce wannan zargi ya fara bayyana ne a shekara ta 2024, cewa ya ci zarafi ta lalata na karamar abokiyar aikinsa.

    Karim Khan ya jagoranci kotun tsawon shekara biyar, wanda a cikin wannan lokaci, kotun ta bayar da sammacin kama mutane da dama da suka haɗa da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, da wasu jami'an ƙungiyar Hamas, da Shugaban Rasha Vladimir Putin, da tsohon shugaban Philippines Rodrigo Duterte.

    Tsige Khan na zuwa ne a wani lokaci da kotun ta duniya ke fuskantar ƙalubale, sakamakon matakan Amurka na neman raunana ikonta.

  9. Majalisar Iran ta ayyana ajandar zaman mako-mako karon farko cikin makonni

    Majalisar Dokokin Iran ta fitar da abubuwan da za ta tattauna a zaman mako-makon da za ta gudanar karon farko cikin makonni bayan dakatarwar da ta biyo bayan yaƙin baya-bayan nan.

    Zaman, wanda aka tsara zai fara ranar Lahadi har zuwa Talata, zai mayar da hankali kan muhimman batutuwan da suka shafi dokoki da manufofin ƙasar.

    Kafofin watsa labaran Iran sun ruwaito cewa daga cikin abubuwan da ke cikin ajandar akwai nazarin wani ƙudirin gaggawa kan tunkarar laifukan ƙasa da ƙasa da kuma duba wani shiri na tallafa wa wasu manufofi.

    Kamfanin dillancin labaran ISNA ya ce wannan ne zaman farko tun bayan fara yaƙin da wakilan majalisar za su samu damar gudanar da ayyukan dokoki da tattaunawa kan sababbin ƙudirori.

    A makonnin da suka gabata, majalisar ta yi gyara ga dokokinta na cikin gida domin ba da damar gudanar da zaman ta intanet.

  10. An umarci jami’an ƴansanda su ɗauki mataki kan masu riƙe da makamai ba bisa ƙa’ida ba

    Sufeto Janar na ƴanSandan Najeriya, Olatunji Disu, ya umarci jami’an ‘yan sanda a faɗin ƙasar su ɗauki mataki mai tsauri kan duk wanda aka samu da makamai ba bisa ƙa’ida ba.

    Ya ce jami’an su yi amfani da tanadin dokar aiki ta Force Order 327 wajen tunkarar masu laifi domin daƙile hare-hare da kuma dawo da zaman lafiya musamman a Jihar Benue.

    Disu ya bayar da umarnin ne a wani taron tattaunawa da ya yi da Gwamnan Jihar Benue, Hyacinth Alia, a Makurdi, yayin wata ziyarar aiki da ya kai jihar sakamakon yawaitar kashe-kashe da hare-haren da ake fuskanta.

    Mahalarta taron sun bayyana damuwa kan hare-haren da ake kai wa tare da tambayar dalilin da ya sa wasu barazanar tsaro ke ci gaba duk da bayanan sirri da ake bai wa hukumomi.

    Sufeto Janar ɗin ya kuma buƙaci matasan jihar Benue su ƙara haɗa kai da ‘yansanda wajen tattara bayanan sirri da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka.

    A nasa ɓangaren, Gwamna Alia ya sake kira da a kafa ‘yan sandan jihohi domin taimakawa wajen magance matsalar tsaro.

  11. Tinubu ya buƙaci likitocin Najeriya da ke ƙasashen waje su dawo gida

    Shugaba Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga likitocin Najeriya da sauran ƙwararrun ma’aikatan lafiya da ke aiki a ƙasashen waje da su dawo gida domin bayar da gudunmawarsu wajen inganta harkokin lafiya a ƙasar.

    Tinubu ya bayyana hakan ne lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar Ƙungiyar Likitocin Najeriya da ke ƙasashen waje tare da shugaban Hukumar ‘Yan Najeriya Mazauna Ƙasashen Waje (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, a Abuja.

    Ya ce Najeriya na buƙatar ilimi, ƙwarewa da gogewar ‘yan ƙasar da suka yi fice a ƙetare domin gina ingantaccen tsarin kiwon lafiya da zai amfani kowa da kowa.

    Shugaban ya yaba wa likitoci ƙasar bisa ayyukan jin ƙai da suka gudanar a sassa daban-daban na ƙasar, inda suka samar da ayyukan jinya, tiyata, shawarwari kan lafiya da sauran tallafin ceton rayuka.

    Ya kuma jaddada cewa gwamnatin sa na ci gaba da aiwatar da gyare-gyare a ɓangaren lafiya tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da ƙwararrun ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje domin rage ƙaurar ƙwararru da bunƙasa ɓangaren kiwon lafiya.

  12. Iran ta fitar da gangar ɗanyen mai miliyan 73 a wata ɗaya

    Iran ta samu damar fitar da kusan gangar danyen mai miliyan 73 daga yankin da takunkuman Amurka suka yi wa katanga cikin kusan wata guda, bayan da Washington ta ɗan sassauta wasu takunkumai da ƙuntatawar da ta sanya kan sayar da man ƙasar.

    Daga ƙarshen watan Yuni zuwa tsakiyar watan Yuli, jiragen dakon mai na Iran da dama sun fara bayyana a ruwan gabashin Malaysia suna kan hanyarsu zuwa kasuwannin Asiya.

    Kamfanin Kepler mai bibiyar jigilar makamashi ya shaida wa BBC cewa man da aka fitar a wannan lokacin na iya kai wa darajar kusan dala biliyan shida.

    Sai dai duk da wannan gagarumar fitar da mai, rahotanni sun nuna cewa manyan masu sayen man Iran a China sun rage sayayyarsu.

    Sai dai Amurka ta janye sassaucin takunkuman da ta yi wa Iran a ranar 7 ga Yuli, bayan ta amince na ɗan lokaci da sayar da ɗanyen man ƙasar tun daga 21 ga Yuni."

  13. Iran ta ce za ta kare kanta daga barazanar Amurka

    Iran ta bayyana cewa ta ƙuduri aniyar kare muradunta da tsaron ƙasarta tare da hana Amurka amfani da Mashigar Hormuz wajen yin barazana ga tsaronta.

    Ministan harkokin wajen ƙasar, Abbas Araghchi, ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da takwaransa na Rasha, Sergei Lavrov, a gefen taron Majalisar Ministocin Harkokin Wajen ƙasashen mambobin Ƙungiyar Haɗin Kan Shanghai (SCO) da ake gudanarwa a Kyrgyzstan.

    A cewar kafofin watsa labaran Iran, Araghchi ya ce rashin tsaron da ake fuskanta a yanzu a Mashigar Hormuz “sakamako ne kai tsaye na karya alƙawarin da Amurka ta yi.”

    Ya ƙara da cewa Iran ta nuna muhimmancin diflomasiyya a harkokin ƙasa da ƙasa, amma a lokaci guda za ta ci gaba da kare muradunta da tsaron ƙasarta daga duk wata barazana.

    A wani ɓangaren kuma, Araghchi ya tattauna ta wayar tarho da ministocin harkokin wajen Masar da Oman a ranar Alhamis kan abubuwan da suka shafi yankin.

  14. Assalamu alaikum

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye wanda ke kawo muku labaran duk muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da saurarn sassan duniya a wannan rana ta Asabar.

    Aisha Babangida ke sake fatan kasancewa da ku a wannan lokaci.

    Za kuma ku iya yin tsokaci a shafukanmun na sada zumunta: facebook, X, instagram, YouTube sai kuma zaurenmu na WhatssApp.