KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran al'amuran da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na ranar Lahadi 06/09/2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Iran ta ce ta kai hari kan jirgin Amurka a mashigar Hormuz

    Iran

    Asalin hoton, Reuters

    Dakarun Juyin Juya Hali na Iran sun ce sojojin su sun kaiwa wani jirgi maras matuki na Amurka hari a daidai mashigar Hormuz.

    Harin ya afku sa’o’i ƙalilan bayan rundunar sojin Iran ta yi barazanar ramuwar gayya, idan sojojin Amurka suka ci gaba da kaiwa jiragen ruwan Iran hari.

    Gargadin ya biyo bayan harin da Amurka ta kaiwa tankokin man Iran 3 ranar Asabar. Amurka ta bayyana cewa hare-haren da ta kai na matsayin martanin harba makamai masu linzami da Iran ta yi kusa da jiragen ruwa na Amurka.

  2. Buɗewa

    Masu bibiyarmu barka da safiyar ranar Lahadi daga nan sashen Hausa na BBC.

    Yau ma mun dawo kamar kullum da labarai da rahotanni da sharhi kan muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya.

    Da fatan za ku ci gaba da kasance da wannan shafi na kai tsaye na sashen Hausa na BBC. Ka da ku manta za ku iya leƙawa sauran shafukan namu na sada zumunta domin samun ƙarin labarai da rahotanni da ma hirarraki.