'Trump bai so ya sake kai wa Iran hari ba'

Asalin hoton, Getty Images
Wasu jami’an gwamnatin Amurka sun ce shugaban ƙasar, Donald Trump, bai amince da buƙatar kai wa Iran harin ramuwar gayya ba sai da safiyar ranar Talata, kamar yadda ɗan jaridar Wall Street Journal, Alex Ward, ya ruwaito.
A safiyar ranar Talata, Trump ya shaida wa Jaridar Wall Street Journal cewa harbo jirgin yaƙin Apache da Iran ta yi "ba wani babban al’amari ba ne", domin matuƙan jirgin sun tsira ba tare da sun samu raunuka ba.
Sai dai rahoton ya ce daga baya shugaban ya sauya ra’ayinsa ne bayan Ministan Tsaron Amurka, Pete Hegseth, da shugaban rundunar hafsoshin tsaron ƙasa, Janar Dan Caine, sun ba shi shawarar ɗaukar matakin soja a wani taro da aka gudanar a Fadar White House.
Daga ƙarshe, Trump ya amince da kai hare-hare kan wasu wurare a Iran a matsayin martani ga harbo jirgin yaƙin Apache, a cewar jami’an Amurka.
Rahoton ya kuma ce bayan waɗannan hare-hare, rundunar juyin juya halin Iran da sojojin ƙasar sun ƙaddamar da sabbin hare-hare kan sansanonin sojojin Amurka da ke yankin.













