Isra'ila za ta faɗaɗa hare-harenta a Lebanon - Netanyahu

Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya jaddada cewa ƙasarsa na shirin ƙara tsananta hare-harenta a Lebanon.
Wakilin kamfanin dillanci labarai na AFP a Nabatieh ya ce harin da aka kai ranar Talata ya janyo turnuƙewar hayaƙi a sassa da yawa na birnin.
Kafar yaɗa labaran kasar ta ruwaito cewa daya daga cikin hare-haren an kai shi ne kusa da asibitin gwamnati kuma ya janyo mummunar barna a wasu yankunan asibitin.
Isra’ila ta faɗaɗa hare-harenta zuwa Kudancin Lebanon, dakarun Hezbollah sun sanar da sun yi taho mu gama da dakarun Isra’ila da suka yi yunƙurin kwace birnin Nabatieh.



























