Amurka ta kai 'hare-haren martani' kan Iran

Asalin hoton, Getty Images
Sojojin Amurka sun ce sun kai hare-hare kan wuraren samar da jirage marasa matuƙa na Iran a birnin Goruk da kuma tsibirin Qeshm a ƙarshen mako.
Rundunar sojin Amurka a gabas ta tsakiya ta bayyana a shafinta na sada zumunta cewa an kai hare-haren ne a matsayin martani ga abin da ta kira “Matakan tsokana daga Iran”, waɗanda suka haɗa da harbo wani jirgin leƙen asiri marar matuƙi na Amurka, wanda take ikirarin yana shawagi ne a sararin samaniyarta.
A matsayin martani, dakarun juyin juya halin Musulunci na Iran sun ce sun kai hari kan wani sansani da sojojin Amurka ke amfani da shi, sai dai ba su bayyana sunan sansanin ba.
Tun da fari, Kuwait ta ce ta dana garakuwar tsaron sararin samaniyarta, don harbo wani makami mai alinzamia da Iran din ta harba.













