Misra ta yi kira ga Iran da Amurka da su cimma yarjejeniya
Misira ta yi kira ga Iran da Amurka da su yi amfani da “damar da ake da ita a yanzu” don cimma yarjejeniya da za ta kawo ƙarshen yaƙin da suke yi.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Misira ta bayyana wannan kira a cikin wata sanarwa bayan Shugaban Amurka Donald Trump ya janye barazanar ci gaba da kai hare-hare kan Iran.
Masu sharhi kan al'amuran da suke da masaniya kan halin da ake ciki sun zayyana wasu abu guda huɗu da suka ce su ne ke tarnaƙi ga cimma sulhu tsakanin Iran da Amurka.