Majalisar Dokokin Najeriya ta buƙaci gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su gaggauta aikin kuɓutar da ɗalibai da malamansu da aka sace a jihohin Oyo da Borno.
Kiran na zuwa ne yayin da ake ci gaba da nuna damuwa kan yawaitar satar dalibai a fadin ƙasar.
Majalisar Wakilai ta ce lamarin na ƙara zama barazana ga ilimi da rayuwar yara, yayin da Majalisar Dattawa ta jaddada buƙatar ƙara tsaurara matakan tsaro a makarantu domin hana sake faruwar irin wannan abu.
A halin da ake ciki, Ƙungiyar Malaman Makaranta ta Najeriya (NUT) ta gudanar da zanga-zanga a wasu jihohi, tana neman gwamnati ta ceto daliban cikin gaggawa.
Sanata Ali Ndume, a wata hira da BBC, ya tabbatar da cewa halin da ake ciki yana da matuƙar tayar da hankali, musamman ga iyalan waɗanda abin ya shafa.
Ya ce ya tattauna da wasu ‘yan majalisa kuma an gabatar da ƙuduri a Majalisar Wakilai kan yaran da aka sace daga Borno tun ranar 15 ga watan Yuni.
“Har yanzu muna da kusan mutane 416 a hannun ‘yan ta’adda da aka ɗauke daga Gwashe, kuma abin ya kai kusan watanni uku,” in ji Ndume, yana mai ƙara da cewa akwai ƙananan yara masu shekaru biyu zuwa uku a cikin waɗanda aka sace.
"Abun shine, sai an samu fili ake shanya, wato ƴan ta'adda da masu sace mutane suna cin karensu ba babbaka shiyasa suke ci gaba kuma abin yana faɗaɗawa, yanzu abun ya zama kamar aikin samun kudi ne."
Ya bayyana cewa rashin tabbas kan rayuwar yaran na ƙara jefa iyalai cikin tashin hankali.
Ndume ya ce dole gwamnati ta ɗauki mataki mai ƙarfi, yana mai cewa akwai buƙatar ƙara jajircewa domin daƙile matsalar da ta daɗe tana ƙara muni.
“Idan aka dage da gaske, za a iya shawo kan wannan matsala,” in ji shi, yana mai ɗora alhakin abin kan gwamnati da hukumomin da ke da alhakin aiwatar da tsaro.
Ya kuma yi gargadin cewa rashin kulawa na ƙara ba wa masu satar mutane damar ci gaba da aikata laifuka kamar wata hanyar samun kuɗi.