DSS ta nemi a ɗage shari’ar Sowore zuwa bayan zaɓen shugaban ƙasa na 2027
Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Najeriya (DSS) ta umarci lauyanta, Akinlolu Kehinde (SAN), da ya nemi a ɗage shari’ar da ake yi wa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar AAC, Omoyele Sowore, kan zargin aikata laifukan intanet har bayan zaɓen shugaban ƙasa na 2027 kamar yadda Gidan talabijin na Channels ya ruwaito.
A cewar wata majiya mai masaniya kan lamarin, an ɗauki matakin ne domin bai wa Sowore damar gudanar da yaƙin neman zaɓensa ba tare da shari’ar kotu ta hana shi gudanar da harkokinsa na siyasa ba.
DSS ta shigar da ƙarar ne bayan wasu saƙonnin da Sowore ya wallafa a shafukansa na X da Facebook a watan Agustan 2025, inda ya kira Shugaba Bola Tinubu da suna “mai laifi”.
Sai dai Sowore ya musanta zarge-zargen da ake masa, yana mai cewa shari’ar na da alaƙa da siyasa kuma an ƙaddamar da ita ne domin takaita masa ‘yancin faɗar albarkacin baki.
Rahotanni sun ce shugaban DSS, Tosin Ajayi, ya yi wata ganawa da jami’an sashen shari’a na hukumar inda aka yanke shawarar neman ɗage shari’ar bayan da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ba da damar fara yakin neman zaɓen 2027.