Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Laraba 10/09/2026

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed da Rabi'atu Runka

  1. Harin Iran a Jordan ya lalata jiragen yaƙin Amurka 20

    Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan sansanin sojin sama na Muwaffaq Salti da ke Jordan da safiyar Laraba.

    Tashar labarai ta CBS News ta Amurka, abokiyar hulɗar BBC, ta ruwaito cewa harin ya yi sanadin lalacewar wasu jiragen yaƙin sojin Amurka da ke sansanin.

    Rahotanni sun nuna cewa kusan jiragen yaƙi kirar F-15 guda takwas sun samu ƙananan matsaloli sakamakon harin.

    Majiyoyi sun ce bayan an gyara jiragen, an mayar da su aiki cikin rundunar sojin saman Amurka.

    Haka kuma, majiyoyin sun ce wani jirgin yaƙi kirar A-10 Thunderbolt, wanda aka fi sani da "Warthog", ya yi matukar lalacewa bayan makami mai linzami ya faɗa masa, lamarin da ya lalata ɗaya daga cikin fika-fikansa gaba ɗaya.

    Wata majiya daga ɓangaren leƙen asiri da ta tattauna da CBS News ta ce babu wani sojan Amurka da ya rasa ransa a harin.

    Sai dai saboda muhimmancin lamarin, majiyoyin sun buƙaci a sakaya sunayensu.

    Rahoton ya kuma ce dakarun Amurka da ke Jordan sun harba sama da makamai masu linzami na kariya kirar Patriot guda 30 a matsayin martani ga harin na Iran.

    Kafin wannan hari, Amurka ta bayyana cewa ta kai hare-hare kan tankokin jigilar man fetur na Iran guda biyar.

  2. Yaushe Afirka za ta sake samun Ballon d'Or?

    Afirka ta taɓa samun wanda ya lashe kyautar Ballon d'Or sau ɗaya kacal, kuma akwai yiwuwar a tsawaita jiran wanda zai yi koyi da George Weah bayan da aka bayyana sunayen ƴan takarar kyautar na wannan shekarar.

    Kyaftin ɗin Morocco Achraf Hakimi da ɗan wasan gaban Senegal Sadio Mane su ne sunayen ƴan wasa biyu na nahiyar da ke cikin jerin ƴan wasa 30 da ka iya lashe kyautar bana.

    Ƴan wasan biyu a baya sun taɓa samun matsayi na ƴan wasa shida na farko cikin jerin manyan ƴan wasa da ke neman Ballon d'Or, amma bayan samun shekarar da Spain ta lashe gasar cin kofin duniya ta Fifa kuma Kylian Mbappe ya zura ƙwallaye 10 inda ya zama gwarzon ɗan wasan da ya fi zura ƙwallaye a gasar, damar ɗan wasan baya na Paris St-Germain ko kuma ɗan wasan gefe na Al-Nassr su ɗauki wannan shaharren kofin ta yi matuƙar raguwa.

    Kuma ba wannan ne karo na farko da Afirka ta gaza yin babban tasiri ba.

  3. Gobara ta yi sanadin mutuwar dalibai 15 a gabashin Congo

    Gobara ta tashi a wurare daban daban a birnin Bukavu da ke gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kwango, inda rahotanni suka ce ta kashe aƙalla ɗalibai 15 tare da jikkata wasu da dama.

    Kafofin yaɗa labarai na cikin gida sun ce ɗaya daga cikin gobarar ta tashi ne a wata makarantar firamare.

    Bidiyoyin da ke yawo a intanet sun nuna yara da aka kai asibiti suna kwance a ƙasa cikin mawuyacin hali. Gobarar ta kuma shafi gidaje.

    Ƙungiyar ƴan tawayen M23 ce ke iko da Bukavu, kuma wani mai amfani da shafukan sada zumunta ya yi zargin cewa kungiyar ba ta ɗauki wani mataki na taimakawa ba.

  4. Aljeriya ta yanke dangantakar diflomasiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa

    Aljeriya ta yanke hulɗar diflomasiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), tana mai zargin ƙasar da aiwatar da matakai "na tsokana da ƙiyayya".

    A cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters, Aljeriya ba ta bayyana takamaiman waɗannan matakan da take zargi ba.

    Jim kaɗan bayan sanarwar Aljeriya, mai ba shugaban ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa shawara kan harkokin diflomasiyya, Anwar Gargash, ya rubuta a shafin X cewa dangantakar diflomasiyya ya kamata ta ginu ne kan "hikima, sadarwa da bayyana muradu a sarari", ba kan "alamomi da ishara masu buƙatar fassara" ba.

    Dangantaka tsakanin ƙasashen biyu ta ƙara tsami a cikin 'yan shekarun nan, inda kafafen yaɗa labarai na Aljeriya suka dinga sukar UAE tare da zargin ta da ƙoƙarin haddasa rikice-rikice a yankin.

    Ma'aikatar Harkokin Wajen Aljeriya ta bayyana cewa ayyukan UAE sun kai matakin da ba za a iya ɗaukar su a matsayin abin karɓa ko jurewa ba, kuma Aljeriya ta"gama amfani da duk hanyoyin da za a bi domin ci gaba da kare dangantakar ƙasashen biyu."

    A nata ɓangaren, Anwar Gargash, ba tare da ambaton Aljeriya kai tsaye ba, ya ce nasarar diflomasiyya tana dogara ne da bayyana matsayi a sarari da kuma gudanar da muradu da saɓanin ra'ayi yadda ya kamata.

    A cewar Ma'aikatar Harkokin Wajen Aljeriya, an gayyaci jakadan UAE zuwa ma'aikatar, inda aka sanar da shi wannan mataki tare da ba shi wa'adin sa'o'i 48 domin aiwatar da shi.

  5. Ƴan Houthi sun ƙwace tsibirin Zuqar a Kudancin Tekun Bahar Maliya

    Kamfanin dillancin labarai na AFP, yana mai nakalto wata majiya ta soji, ya ruwaito cewa mayaƙan Houthis sun ƙwace tsibirin Zaqr (Zuqar) da ke kudancin Tekun Bahar Maliya.

    Wannan dai ya biyo bayan kai hare-haren rokoki da kuma mamayar ƙasa ta hanyar amfani da kwale-kwalen da ke ɗauke da mayaƙa.

    Kamfanin dillancin labaran ya kuma nakalto shaidu suna cewa a ranar Alhamis mayaƙan Houthi sun shiga birnin tashar jiragen ruwa na Mokha (Mocha) suna rera taken:"Mutuwa ga Amurka, Mutuwa ga Isra'ila."

    AFP ta ce rikicin da ake gwabzawa a Yemen ya yi sanadin mutuwar sama da mutum 500 tun daga makon da ya gabata, inda mafi yawansu mayaƙa ne.

    Haka kuma, ƙungiyar da ke kula da masu ƙaura ta duniya ta bayyana cewa kusan mutum 20,000 sun tsere daga gidajensu sakamakon faɗan.

  6. Mutane 20 sun mutu a gobarar jirgin ruwa a China

    Akalla mutane 20 ne suka mutu bayan da gobara ta tashi a wani jirgin dakon kaya mai tutar wata ƙasar waje da ke tashar jiragen ruwa a birnin Qingdao da ke gabashin China, a cewar gidan talabijin na ƙasar, CCTV.

    CCTV ta ce mutane 42 ne ke cikin jirgin, inda aka ceto 17 daga cikinsu. Mutane biyar daga cikin waɗanda aka ceto suna asibiti.

    Shugaban China, Xi Jinping, ya yi kira da a ƙara ƙoƙarin ceto mutanen da abin ya rutsa da su, yayin da Firaminista Li Qiang ya buƙaci a ceto waɗanda suka makale tare da yin taka-tsantsan don hana faruwar wasu bala'o'i.

    Gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 11:15 na safe agogon China, yayin da ake aikin gyaran jirgin a wani wurin gyaran jiragen ruwa. CCTV ta ce an shawo kan gobarar bayan fiye da sa'o'i uku.

    Hotunan kafafen yaɗa labaran China sun nuna jirgin mai tsawon mita 190, wanda ke ɗauke da tutar Liberia kuma ya isa Qingdao a ranar 31 ga Agusta.

    Gobarar ta faru ne kusan wata guda bayan wata fashewa a wani wurin gyaran jiragen ruwa a lardin Fujian, inda ma'aikacin ceto ɗaya ya mutu, wasu 12 kuma suka jikkata.

  7. Wani ɗan jarida ya zama sarki a Uganda

    An zaɓi wani mai gabatar da labarai a talabijin a Uganda domin hawa karagar mulkin masarautar gargajiya ta Tooro da ke yammacin ƙasar.

    Yarima Edward Rukidi Kijanangoma, wanda ke aiki a gidan talabijin na gwamnati, UBC, zai gaji ɗan uwansa na kusa, Sarki Oyo Nyimba, wanda ya rasu a watan jiya sakamakon cutar daji yana da shekara 34.

    Duk da cewa Uganda jamhuriya ce, a hukumance ƙasar na amincewa da masarautun gargajiya, waɗanda galibi ke taka rawa ta al'adu kuma suke da ƙarancin ikon siyasa.

    Ana sa ran za a yi jana'izar marigayi sarkin a jibi Asabar.

  8. Amurka za ta aika wa Najeriya kayan aikin soja

    Amurka ta ce za ta aika wa Najeriya wasu kayan aikin soja, yayin da ƙasashen biyu ke ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa wajen yaƙi da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi da sauran barazanar tsaro.

    Rundunar sojin Amurka da ke kula da nahiyar Afirka (AFRICOM) ta ce wani jirgin sama na rundunar sojin saman Amurka kirar C-17 ne zai kai kayan aikin ga rundunar sojin saman Najeriya a ƙarshen wannan mako.

    A cewar AFRICOM, kayan aikin wani ɓangare ne na yarjejeniyar sayar da kayayyakin soji tsakanin ƙasashen biyu, wadda ke ƙara ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Amurka da Najeriya, tare da taimakawa ƙoƙarin Najeriya na yaƙi da ta'addanci a yankin.

    Isar da kayan aikin na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke ƙara ƙaimi wajen yaƙi da masu tayar da ƙayar baya na masu iƙirarin jihadi da kuma ƴan bindiga da sauran barazanar tsaro.

    Kodayake rundunar sojin Najeriya ta samu wasu nasarori a watannin baya-bayan nan, hare-hare da sace-sacen mutane domin neman kuɗin fansa na ci gaba a wurare da dama.

    Najeriya da Amurka sun kuma ƙara haɗin gwiwa a fannonin musayar bayanan sirri, horas da jami'an tsaro da kuma ba da tallafin soja.

    A watan Janairu ne dakarun Amurka suka kai wasu kayayyakin soja Najeriya, inda suka ce matakin na tallafa wa ayyukan tsaron da ƙasar ke gudanarwa, tare da nuna irin dangantakar tsaro da ke tsakaninsu.

    Kimanin sojojin Amurka 200 da aka tura Najeriya a farkon shekarar nan domin wani aikin yaƙi da ta'addanci sun janye bayan kammala aikinsu.

    Sai dai haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen biyu na ci gaba.

    Daga cikin horon da Amurka ta bayar a baya-bayan nan a Najeriya akwai yadda ake sarrafa jirage marasa matuƙa, dabarun yaƙi da abubuwan fashewa da kuma kula da waɗanda suka jikkata a filin daga.

  9. Fiye da yara miliyan ɗaya sun koma makaranta a Najeriya

    Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, ya ce fiye da yara miliyan ɗaya da ba sa zuwa makaranta sun koma ajujuwa cikin watanni 20 da suka gabata.

    Ya kuma ce kusan yan mata miliyan shida da dubu dari bakwai sun amfana da shirye-shiryen da aka ƙaddamar domin ƙara yawan yaran da ke shiga makaranta da kuma rage yawan waɗanda ke barin karatu.

    Alausa ya bayyana hakan a Abuja yayin da yake karɓar wakilin UNESCO a Najeriya, Farfesa Isaiah Barreto Da Rosa, wanda ya kai masa ziyara.

    Ministan ya buƙaci ƙara haɗin gwiwa da UNESCO domin tallafa wa shirin sauya fasalin ilimi na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

    Ya ce shirin gwamnatin ya fi mayar da hankali kan fannoni shida, da suka haɗa da koyar da sana'o'i da yadda za a yi amfani da kirkirarriyar basira ta AI, da dawo da yaran da ba sa zuwa makaranta, ilimin ’ya’ya mata da kuma tabbatar da ingancin ilimi.

    Ministan ya kuma ce gwamnati na saka hannun jari wajen inganta ƙwarewar malamai, inda suke da burin horas da malamai miliyan ɗaya. Ya kuma yi kira da a ƙara mai da hankali kan ilimin yara maza, tare da ci gaba da samun nasarorin da aka samu wajen ilimin ’ya’ya mata.

  10. 'Mayaƙan Houthi sun ƙwace iko da tashar jiragen ruwan Mokha a Yemen'

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito, ya ambato jami'an gwamnatin Yemen uku na cewa mayaƙan tawayen Houthi sun ƙwace iko da tashar jiragen ruwa ta Mokha.

    Mayaƙana na Houthi na ƙoƙarin karɓe iko da muhimman tashoshin jiragen ruwa da ke gaɓar Tekun Bahar Maliya, wani mataki da zai ƙara musu ƙarfin iko a mashigar Bab al-Mandab, mai matuƙar muhimmanci ga zirga-zirgar jiragen ruwa na duniya.

    Tun da farko, mummunar arangama tsakanin dakarun da Saudiyya ke mara wa baya da mayaƙan Houthi a Yemen ta haifar da fargabar yiwuwar yaƙin ya ƙara faɗaɗa.

    Haka kuma jiragen yaƙin Saudiyya sun kai hare-hare a wurare da dama na Yemen, a matsayin martani ga hare-haren da aka kai kan muhimman cibiyoyinsu da kayayyakin more rayuwa.

    Ƙaruwar rikicin ya sa hukumomi ayyana dokar ta-ɓaci a birnin Khamis Mushait da ke kudu maso yammacin Saudiyya.

  11. Amurka ta kai hari kan wani jirgin ruwa a tekun Caribbean

    Sojojin Amurka sun ce sun sake kai hari kan wani ƙaramin jirgin ruwa da ake zargin yana safarar miyagun ƙwayoyi a yankin tekun Caribbean, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum uku.

    Rundunar sojin Amurkar ta wallafa wani bidiyo a kafafen sada zumunta wanda ke nuna lokacin da wani ƙaramin jirgi ya tarwatse sakamakon harin.

    Sojojin sun bayyana mutanen da aka kashe a matsayin “'yan ta'addan safarar miyagun ƙwayoyi”, sai dai ba su gabatar da wata hujja da za ta tabbatar da zargin ba.

    Tun da farko, a yayin wata ziyara da ya kai Ecuador Sakataren Harkokin Wajen Amurka, ya kare manufar Washington ta kai hare-haren da ke hallaka waɗanda ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi ta ruwa, yana mai cewa hakan ya zama wajibi domin hana ƙungiyoyin masu aikata laifuka durƙusar da ƙasashen Kudancin Amurka. Sai dai ƙungiyoyin kare haƙƙin bil adama sun yi Allah-wadai da irin waɗannan hare-hare, suna masu cewa suna kama da kisan gilla.

  12. Za a gurfanar da iyayen yaran da ba sa zuwa makaranta a Nasarawa

    Gwamnatin Jihar Nasarawa ta umarci hukumar ilimi ta bai-ɗaya ta jiha (SUBEB) da ta fara wayar da kan jama'a domin mayar da yaran da suka kai shekarun makaranta amma ba sa zuwa makaranta aji.

    Gwamnatin ta ce tana shirin kafa kotunan tafi-da-gidanka domin gurfanar da iyayen yaran da aka samu suna yawo a tituna a lokacin karatu.

    Babban mataimaki na musamman ga Gwamna Abdullahi Sule kan harkokin jama'a, Peter Ahemba ne ya bayyana hakan a Lafia a ranar Laraba.

    Ya ce SUBEB za ta yi aiki tare da ma'aikatar shari'a wajen duba yadda za a kafa kotunan, amma za a fara da wayar da kai kafin fara aiwatar da matakin.

    Ya ce daga bisani za a kafa wata tawaga da za ta gano yaran da ke yawo a lokacin makaranta tare da bibiyar iyayensu domin gurfanar da su idan ya zama dole.

    Gwamnati ta kuma tanadi kayan makaranta sama da 10,000, ciki har da littattafan rubutu, kayan makaranta da takalma, domin rabawa ɗalibai.

    Ahemba ya kuma ce jihar ta kammala ɗaukar malaman makarantun firamare 1,000, waɗanda za a tura musamman zuwa makarantun karkara. Ya ce an ɗauke su ne bisa cancanta daga cikin sama da mutane 10,000 da suka nemi aikin.

  13. Lokacin da aka fi fuskantar tsananin zafi a Turai

    Hukumar kula da sauyin yanayi ta Tarayyar Turai, Copernicus, ta ce watan Agusta na bana ya kasance daya daga cikin watannin da suka fi zafi a tarihi, inda daga shi sai kuma watan Yuli na 2023.

    A cewar hukumar, matsakaicin yanayin zafin da aka auna a dukkan watannin biyu ya kai digiri 1.65 a sama da matakin da ake da shi kafin juyin juya halin masana’antu, wanda ya zarce iyakar digiri 1.5 da masana ke gargadin cewa wucewar hakan na ƙara haɗarin afkuwar matsanancin yanayi kamar ambaliyar ruwa, fari da matsanancin sauyin yanayi.

    Masana sun ce babban abin da ke haddasa hauhawar yanayin zafin duniya shi ne ci gaba da amfani da makamashi mai gurbata muhalli.

    Sun kuma bayyana cewa wannan matsala na ƙara tsananta saboda ƙaruwar ƙarfin matsalar sauyin yanayi ta El Niño, wanda ke haifar da dumamar ruwan tekun Pasifik. Hakazalika, hukumar ta kula da yanayi ta Turai ta ce lokacin bazara na bana a Yammacin Turai ya kasance mafi zafi da aka taɓa gani a tarihin bayanan da ake da su.

  14. Kamfanin Apple ya fito da sabuwar iPhone kan dala 2,000

    Kamfanin Apple ya fito da wata sabuwar wayar iPhone mai dauke da sabon salo şabanın abin da aka saba gani bayan kusan shekaru 20 da ƙaddamar da wayar ta farko.

    Sabon shugaban kamfanin John Ternus, wanda ya maye gurbin Tim Cook, ya gabatar da sabon iPhone mai budewa da rufewa mai suna Duo a wani taron shekara-shekara na kamfanin da aka budanar a ranar Laraba.

    Wayar tana buɗewa kamar littafi kuma ita ce iPhone mafi girma da aka taɓa ƙerawa. Farashinta a Amurka yana farawa daga dala $1,999, kuma zai iya kaiwa $3,200, yayin da farashinta a Birtaniya yake farawa daga £1,999.

    Ternus ya ce an ƙirƙiri Duo ne ta hanyar la'akari da tasirin wayar kamfanin ta iPad, inda ya ce waya mai budewa da rufewa tana da sauƙin amfani.

    Idan aka buɗe wayar, tana kama da ƙaramin iPad, yayin da idan aka rufe, tana kama da iPhone mai faɗi.

    Ternus ya shafe shekaru yana aiki a sashen ƙera kayayyakin fasaha na Apple, kuma yana daga cikin mutanen da suka taka rawa wajen samar da sabuwar wayar.

    Sabuwar way ta iPhone za ta taimakawa Apple wajen rage sukar da take sha cewa ba ta ƙaddamar da sabon samfuri na musamman ba, ko kuma waya mai dauke da fasaha mai jan hankali tun bayan iPhone na farko a shekarar 2007.

    Sai dai Dipanjan Chatterjee, manazarci a Forrester, ya yi gargadin cewa Duo na iya zama wata waya mai tsada wadda za ta fi zama abin nuna isa, sama da nuna gagarumar nasarar ci gaban kasuwanci.

    Haka kuma kamfanin ya kuma da iPhone 18 Pro da 18 Pro Max, waɗanda farashinsu a Amurka ya fara daga dala $1,199 da $1,299.

    Apple ta kuma sanar da wasu sabbin fasahohin AI a iPhone 18, inda za ta iya bincika bayanai a cikin wayar mutum, ciki har da saƙonni da email, domin nemo bayanai, amsa tambayoyi da kuma aiwatar da wasu ayyuka a madadin mai sayar.

  15. Me ya sa ake musayar yawu tsakanin magoya bayan Atiku da Kwankwanso?

    A Najeriya, yayin da ake ci gaba da tunkarar babban zaɓen ƙasar na 2027, ka-ce-na-ce sun kaure tsakanin magoya bayan ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC Atiku Abubakar, da ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC Rabiu Musa Kwankwaso.

    Kwankwaso ne dai ya shawarci Atiku da ya janye daga neman shugabancin Najeriya, saboda cewarsa shekaru sun cimma masa.

    Kwankwaso ya bayyana haka ne a lokacin ya karɓi baƙuncin magoya bayan jam'iyyar NDC daga Adamawa, jihar Atiku, inda a cikin jawabinsa ya buƙaci ce su biya su fada wa Atiku cewa ya haƙura da takara, ya koma gefe ya cigaba da riƙe sarautarsa ta Wazirin Adamawa.

    Waɗannan kalamai sun haifar da muhawara a tsakanin magoya bayan ɓangarorin biyu, lamarin da ya ƙara bayyana takun-saƙar da ke tsakanin jagororin siyasar guda biyu.

    Da suke mayar da martani, ɓangaren Atiku sun zargi Kwankwaso da goyon bayan Tinubu ta bayan fage, inda wani mai magana da yawun Atikun, Abdulrasheed Shehu Uba Sharaɗa ya ce ba su yi mamaki ba, domin a cewarsa kamata ya yi Kwankwaso ya haɗa ba Tinubu wajen bayar da shawarar domin shi ma ya koma gefe ya huta.

    Sai dai jigo a NDC, Yusuf Kofar Mata ya yi martani, inda ya ce wannan kalamai na Kwankwaso yabo ne ba suka ba, domin a cewarsa shekaru baiwa ne, kuma mutane suna so Allah ya musu albarka na shekaru.

    Ya ƙara da cewa lallai ya kamata mutane masu shekaru irin su Atiku su koma gefe suna bayar da shawara, domin a cewar Yusuf Ƙofar Mata hakan zai fi kyau.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake cigaba da hanƙoron ganin jam'iyyun hamayya sun dunƙule waje ɗaya domin fuskantar babban zaɓen ƙasar, inda wasu ke tunanin dunkulewar ce za ta taimaka musu domin samun sauƙin fuskantar jam'iyyar APC mai mulki.

    Magoya bayan fitattun ƴan siyasar na arewa sun daɗe suna musayar yawu a kan wane ne ya fi girma da ƙarfi da tarin masoya da ma gogewa a siyasar.

    A watannin baya magoya bayan ɓangarorin biyu sun shiga murna bayan jagororin siyasar biyu sun dunƙule a jam'iyyar ADC domin fuskantar APC, amma sai auren ya ƙi daɗi, inda suka rabu bayan lokaci kaɗan.

    Atiku Abubakar dai shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar ADC, shi kuma Rabiu Musa Kwankwanso shi ne ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a jam'iyyar NDC, inda zai mara wa Peter Obi baya.

    Dangantakar siyasa tsakanin Atiku Abubakar da Rabiu Musa Kwankwaso ta daɗe, domin sun shafe sama da shekara 30 suna gwagwarmayar siyasa, lamarin da ya sa ake tunanin ya kamata su kasance makusantan juna a siyasa.

    Duk da cewa a wasu lokuta sun kasance a jam'iyyu daban-daban ko kuma sun kara da juna a zaɓe, asalinsu na siyasa ya samo asali ne daga tafiya guda, inda dukansu suke da alaƙa da ƙungiyar siyasa ta 'People's Front of Nigeria' ta Marigayi Shehu Musa Yar'adua a Jamhuriya ta uku, wadda ta kasance ɗaya daga cikin ƙungiyoyin siyasa mafi ƙarfi a wancan lokaci, kafin daga baya suka narke a SDP.

  16. Yadda wani jirgin ruwa ya kama da wuta a tsakiyar tekun Philippines

    Hukumar tsaron gabar teku ta Philippines ta ce aƙalla mutum biyar ne suka mutu bayan wata gobara ta tashi a cikin wani jirgin ruwa na fasinja.

    Hukumar ta ce sama da mutum 80 har yanzu ba a gano inda suke ba bayan gobarar da ta rutsa da jirgin MV June Aster, wanda ke kan hanyarsa daga birnin Manila zuwa tsibirin yawon buɗe ido na Coron a lardin Palawan.

    Wakilin BBC ya ce akwai tambayoyi da dama kan yadda irin wannan abu zai faru Wani bidiyo da hukumar tsaron gabar tekun ta wallafa a intanet ya nuna jirgin gaba ɗayansa ya kama da wuta, yayin da ake ciro wasu fasinjoji daga cikin ruwa. Daga baya, hukumar ta bayyana cewa an ceto fiye da mutum 40 daga cikin waɗanda ke cikin jirgin.

  17. Mutum 24 sun mutu a Ondo bayan shan giya

    Akalla mutum 24 ne suka mutu bayan da ake zargin sun sha wata barasa da ake haɗawa a gida a ƙaramar hukumar Odigbo ta jihar Ondo.

    Gwamnatin jihar ta ce ta ƙaddamar da bincike domin gano ainihin abin da ya haddasa mutuwar mutanen, wadanda suka mutu tsakanin ranar 3 zuwa 7 ga watan Satumban 2026.

    Ma’aikatar Lafiya ta jihar ta ce sakamakon binciken farko ya nuna cewa lamarin na da alaƙa da shan ɓarasa da ake hada wa a gida, wanda aka fi sani da “Monkey Tail”.

    Mazauna yankin sun ce wasu daga cikin wadanda suka mutu sun rasu ne a gidajensu, yayin da wasu kuma suka mutu cikin barci.

    Kwamishinan Lafiya na jihar Ondo, Dakta Banji Ajaka, ya ce hukumomi na daukar lamarin da matukar muhimmanci, sai dai yaƙi bayyana taƙamaiman sinadarin da ake zargin ya haddasa mutuwar inda ya ce sai an kammala binciken likitoci da gwaje-gwajen dakin bincike.

    A halin yanzu, shugaban karamar hukumar Odigbo, Taiwo Adegoroye, ya sanya dokar hana sayarwa da shan barasa da ake haɗa wa a gida na tsawon wata guda a yankin, a matsayin matakin kariya.

    Adegoroye ya ce wani bincike na farko da ma’aikatan lafiya na karamar hukumar suka gudanar, wanda ya hada da tambayoyi kan yanayin mutuwar wadanda abin ya shafa, ya nuna yiwuwar alaka tsakanin mace-macen da shan wasu abubuwan da ake samarwa a gida.

    Ya ce: “An dauki matakin ne domin kare lafiyar jama’a yayin da hukumomin da abin ya shafa ke ci gaba da bincike kan lamarin.”

    Ya ce ana ci gaba da gudanar da binciken sinadarai masu guba domin gano ainihin abin da ya haddasa mace-macen, tare da gargadin cewa duk wanda aka kama yana sayarwa ko rarraba abubuwan shan da aka haramta a lokacin dokar zai fuskanci kamawa da gurfanar da shi a gaban kotu.

    An gano cewa mace-macen sun faru ne a garuruwan Araromi-Obu, Orita New Town da Odigbo, yayin da wasu mutane da dama ke karbar magani a asibitoci.

  18. Zan ba kowane ɗan Amurka dala 5,000 idan jam'iyyarmu ta samu nasara a zaɓe - Trump

    Shugaban Trump, na Amurka ya ce zai bai wa kowane babba ɗan ƙasar dala 5,000 idan jam'iyyarsa ta Republican ta samu rinjaye a duka majalisun dokokin ƙasar a zaɓukan rabin wa'adi da za a gudanar a watan Nuwamba.

    Sai dai har yanzu babu cikakken bayani kan yadda za a samar da kuɗin da kuma cewa ko hakan bai saba wa doka ba.

    Trump ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron farko na jam'iyyar Republican da aka shirya domin zaɓukan tsakiyar wa'adi, inda ya yi ƙoƙarin ƙarfafa magoya bayansa gabanin zaɓukan da ake kallon suna da matuƙar muhimmanci.

    Ya ce sharadi daya kawai ya ke da shi , shi ne dole ne a kashe kudin a Amurka duk da raguwar amincewar jama'a da shugabancinsa a wasu ƙuri'un jin ra'ayi, shugaban ya buƙaci mahalarta taron da su fito ƙwansu da kwarkwatarsu su kaɗa ƙuri'a, yana mai cewa su yi hakan kamar shi kansa ne ke takara a zaɓen.