Iran da Pakistan na tattauna batutuwan da suka shafi tsagaita wuta
Ministan harkoki ƙasar Iran ya ce sun tattauna batutuwan da suka shafi tsagaita wuta da manyan jami'an ƙasar Pakistan, a daidai lokacin da Pakistan ɗin take shirye-shiryen karɓar baƙuncin tattaunawar ta Iran da Amurka.
Abbas Araghchi, a wata sanarwa a Telegram ya fadi cewa ya tattauna da Ishaq Dar, mataimakin firaiministan Pakistan tare da ministan harkokin Pakistan da kuma Field Marshall Asim Munir.
Ya ƙara da cewa sun yi maganganu dangane da "ci gaban yakin gabas ta Tsakiya mai alaƙa da batun tsagaita wuta.
Aragchi bai fayyace ko yana magana ne dangane da batun tsagaita wutar Iran da Amurka ko kuma ta Isra'ila da Lebanon ko kuma duka biyun.