Sakamakon yadda sauye-sauyen da gwamnatin hugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ta jam'iyyar APC ta kawo a kasar wadanda wasu ke gani sun haifar da wahalahalu na tsanani na rayuwa, wani jigo a jam'iyyar kuma dan majalisar dattawa Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila ya shawarci ƴan jam'iyyar su yi amfani da kalamai na sanin ya kamata da mutuntawa da kuma tausasa harshe wajen yakin neman zaɓen 2027.
Sanatan ya bayyana hakan ne a tattaunawar da ya yi da BBC, yana mai nuni da cewa yadda yan kasar suka fusata da halin tabarbarewar tattalin arziki da tsadar rayuwa to sai an bi su da kalamai na shawo kai.
Danmajalisar Dattawan ya ce ya mika wa kwamitin yakin neman sake zaben Shugaba Tinubu wasu jerin shawarwari da suka shafi rayuwar 'yan Najeriya, wadanda ya ce ya 'yan kwamitin ya kamata su yi amfani da su a aikinsu na kamfe.
Ya yi karin bayani da cewa: ''Na yi kira ga shi Abdul'aziz Abubakar Yari da 'yan kwamitinsa da mu da muka shiga zabe cewa mu gaya wa kanmu gaskiya, mu kalli halin da Najeriya take ciki.''
''Akwai abubuwa guda uku kwarara wadanda dole maganganunmu sai sun nuna a jikinmu mun san wani abin yana faruwa,'' in ji shi.
Ya ce, ''Akwai kalubale na tsaro wanda mutane suna rasa rayuwarsu kuma wasu suna cikin wani yanayi na rashin jin dadi na barin garuruwansu, akwai abin tausayawa. Ga zama a cikin tsoro a bangarori da dama a karkashin jagorancinmu.''
To amma kuma Kawu Sumailan ya kara jaddada irin zargin da ake yi a kan wasu daga cikin 'yan kwamitin yakin neman zaben Shugaba Tinubun na cewa wasunsu da dama suna da kashi a gindinsu, duka da cewa 'yan jam'iyyarsa ne ta APC, inda ya ce:
''Gaskiyar magana da yawa daga cikin mambobin wannan kwamitin su ne matsalar gwamnatin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da APC.''
''Yan jam'iyyarmu amma kowa zai amsa sunan ubansa. Kowa yana komawa gida a zabo shi ya taho.''
Ya ce,'' Kuma dukkan irin wadannan abubuwa mun fada a zaman sirri, mun fada a zaman fili, sannan mun fada wajen 'yan jaridu.''
''Na duba na ga yawan wadanda suke cikin wannan kwamiti sun taimaka kwarai da gaske wajen tsunduma gwamnatin APC da tsunduma gwamnatin Tinubu cikin matsalar da ake kallonta da shi.''
Sanatan mai wakilitar mazabar Kano ta Kudu a majalisar dattawan Najeriya ya yi karin haske da cewa muhimmin aiki da kuma kasancewar gwamnati na farko shi ne ta tabbatar da tsaron rayuwa da mutunci da dukiyar al'ummarta, daga nan kuma sai samar da abubuwa na more rayuwa su biyo baya.
Dangane da hakan ya nuna lalle akwai gazawar gwamnati a wannan bangare na sauke nauyin da ke kan gwamnati a kan al'ummarta.
Ya ce: ''To mutane ba za su gamsu ba matukar ba su ga ko'ina an zauna lafiya ba.Matukar ba su yaba a zahiri sun fito sun ga kokarin da muke yi ba. To duk kokarin da muke yi ya kamata mu tausaya a irin maganganunmu.''
Kawu ya kwatanta shugabanci da yadda likita yake yi wa maras lafiya magani, da cewa likita yana kokarin yi mawa mutum magani yana tausaya masa amma kuma alokaci guda yana yi masa abin da ke sa mutumin ya ji zafi domin ta hakan ne zai samu lafiya.
Ganin cewa Sanatan yana daya daga cikin fitattun 'yan jam'iyyar APC daga Kano wanda kuma ya tsaya takarar sake neman kujerar sanatan da yake kai, ya fito yana nuna cewa lalle akwai matsalar a yadda jam'iyyar za ta tunkari al'ummar Najeriya kan su sake zabenta a 2027 sai ya ce:
''Babu wani abu ai magana ce ta mu gaya wa kanmu gaskiya kuma duk wanda yake bin maganganu na haka ne dole za ka fade su da dadi ba dadi. In ma an ki maganar da muka fada daga baya za a zo a yarda da ita.''
Dangane da yadda 'yan adawa ke ganin APC din ba ta abin da yza ta yi wa 'yan kasar yakin neman zabe da su, sai Kawu Sumaila ya ce:
''Daga daya zuwa goma zan iya lissafa maka 'yan'adawa da suka yi wa Najeriya illar da APC ba ta yi mata ba , kuma idan aka fito da ita tashin hankali ne. Su su ma dawo su shiga zabe abin kunya ne don ba irin karyar da ba su yi wa 'yan Najeriya ba.''
Sanata Kawu ya ce shi dai rokon da zai yi shi ne musamman 'ga Arewacin Najeriya shi ne jama'a su daina duba cewa sai gwamnati ko dan APC ko jami'an tsaro ne za su yi, kowa ya bayar da gudummawarsa a ceto yankin daga halin da yake ciki.