Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Labaran wasannin BBC Hausa daga ranar 19 zuwa 24 ga watan Afrilun 2026

Wannan shafi ne da zai ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa daga ranar Lahadi 19 zuwa Juma'a 24 ga watan Afrilun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. , Daga Jaridu

    Paris St-Germain ta gana da wakilin ɗan wasan Portugal da West Ham Mateus Fernandes. (Foot Mercato - in French)

    Chelsea na ci gaba da shawarar wanda zai maye gurbin Liam Rosenior, yayin da take duba wanda zai maye gurbin sa ciki har da mai horar da yan wasan Bournemouth Andoni Iraola.(RMC Sport - in French)

    Chelsea na kuma duba yiwuwar ɗauko ɗan wasan tsakiya Cesc Fabregas, wanda yanzu ya ke horar da ƴan wasan Como da ke Italiya.(Football Insider)

    Barcelona na sonMarcus Rashford, da ya ci gaba da zama a ƙungiyar a matsayin dan wasan aro a kakar wasanni mai zuwa, maimakon su biya Manchester United fam miliyan 26a matsayin dan wasan su na din-din din. (Mirror)

    Liverpool, da Chelsea, da Tottenham, da Newcastle, da Aston Villa da Newcastle sun nuna sha'awarsu na ɗaukar mai tsaron ragar Manchester City da Ingilan James Trafford.(Goal)

  2. Duk wanda ya sa ran zamu lallasa Burnley bai san ƙwallo ba, Premier League

    Marc Guehi ya ce duk wanda ya yi tunanin Manchester City za ta doke Burnley da tazara ƙwallaye da yawa a wasan da suka yi a daren Laraba, “bai san ƙwallon ƙafa ba”.

    Ƙwallon da Erling Haaland ya ci a minti na biyar ta isa ta bai wa ƙungiyar Pep Guardiola nasara da ci 1-0 a filin Turf Moor, wanda hakan ya sa Burnley ta fadi daga gasar, kuma ya ɗora Manchester City zuwa saman teburin gasar bisa yawan kwallaye da suka ci, inda ta kawo ƙarshen kwanaki 200 da Arsenal ta shafe tana kan jan ragamar teburin, kwanaki uku bayan City ta doke su da ci 2-1 a Etihad.

    Sai dai duk da cewa mutane da dama sun yi tsammanin City za ta ci ƙwallaye da yawa domin ƙara bambancin kwallayenta a fafatawar da take yi da Arsenal a tseren lashe kofin bana.

    Guehi ya ce: “Kowa yana ganin irin waɗannan wasanni masu sauƙi ne, alhali kuwa an yi ƙoƙari sosai a wasan da suka yi da Arsenal a baya.”

  3. , Daga jaridu

    Manchester United na son ɗakar ɗan wasan Bournemouth da Ingila Alex Scott. (Mirror)

    United na matuƙar son ɗauko ɗan wasan Benfica Richard Rois, don in ga ta tsakiyar ƙungiyar. (Caught Offside)

    Bournemouth ta shiga cikin jerin ƙungiyoyin da ke son ɗaukar ɗan wasan Amurka da Bayer Leverkusen Malik Tillman. (Teamtalk)

    Fulham na duba tsarin su na shirin ko ta kwana, kan tafiyar mai horar da ƴan wasan ƙungiyar da kwantaraginsa za ta ƙare a ƙarshen kakar na.(The i)

    Arsenal na sa ido kan ɗan wasan tsakiya na Turkiya Arda Guler, wanda zai iya barin Real Madrid saboda rashin tabbas kan makomar Alvaro Arbeloa. (Caught Offside)

  4. Fifa ba za ta maye gurbin Iran da Italy ba a gasar kofin duniya, Gasar kofin duniya

    Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya, FIFA, ba ta da wani shiri na maye gurbin Iran da Italy a gasar Kofin Duniya ta bana, a cewar wasu majiyoyi, bayan da wani wakili na musamman daga shugaban Amurka Donald Trump suka gabatar da wannan shawara.

    An dade ana samun rashin tabbas kan halartar Iran a gasar, saboda yakin da take yi da Amurka da Isra’ila.

    Wakilin, Paolo Zampolli, ya shaida wa Financial Times cewa: “Na tabbatar na ba Trump da shugaban FIFA Gianni Infantino shawarar cewa Italy ta maye gurbin Iran a Kofin Duniya.

    FIFA ba ta yi magana kai tsaye kan shawarar ba, amma ta nuna wani bayani da Infantino ya yi a makon da ya gabata inda ya ce: “Tawagar Iran za ta buga gasar cin kofin duniya.”

    Rahoton Financial Times ya ce an gabatar da wannan shiri ne domin kyautata alaka tsakanin Amurka da Italiya, bayan da Firayim Minista Giorgia Meloni ta soki Trump kan kalaman da ya yi game da Paparoma Leo XIV.

    Ƙasar Italiya, wadda ta lashe Kofin Duniya sau hudu, ta kasa samun gurbin shiga gasar karo na uku a jere bayan ta sha kashi a wasan neman gurbi a hannun Bosnia and Herzegovina a watan da ya gabata.

    Ana sa ran Iran za ta kara da New Zealand da Belgium a Los Angeles a ranakun 15 da 21 ga watan Yuni, sannan ta kara da Masar Seattle ranar 26 ga watan Yuni.

    Gasar Kofin Duniya, wadda za ta fara ranar 11 ga watan Yuni, za a gudanar da ita ne a ƙasashen Amurka da Canada da kuma Mexico.

  5. Arda Guler da Eder Militao ba za su yi wa Real Madrid sauran wasannin bana ba, Real Madrid

    Ƙungiyar Real Madrid ta fuskanci babban koma baya, sakamakon da Arda Guler da Eder Militao ba za su buga sauran wasannin kakar bana ba, saboda raunukan da suka ji.

    A cewar majiyoyin kungiyar, ana sa ran ƴan wasan biyu za su yi jinya kusan mako hudu, amma za su murmure kafin a fara gasar Kofin Duniya, wadda ta rage kasa da kwanaki 50 a fara.

    Raunin Guler ya ji rauni ne a lokacin atisaye, shi kuwa Militao ya ji rauni a wasan da Real ta ci Alaves 1-0 a La Liga ranar Talata.

    Da yake saura wasa shida a kammala kakar bana, Barcelona ce kan gaba a teburin La Liga da maki 82, inda ta bar Real Madrid ta biyu da maki 73.

    Kungiyoyin biyu za su hadu a wasan El Clasico a Camp Nou ranar 10 ga watan Mayu, inda Barcelona za ta iya lashe kofin karo na biyu a jere idan ta doke Real Madrid, wadda za ta kare kakar nan ba tare da lashe kofi ba karo na biyu a jere..

  6. , Daga Jarida

    Manchester United ta sanar da Portugal Bruno Fernandes, cewar suna son ya ci gaba da zama a Old Trafford. (Sun)

    Sunderland za ta iya korar mai horar da ƴan wasanta Regis Le Bris a ƙarshen kakar nan, idan ya gaza kai ƙungiyar gasar Eroupean. (Talksport)

    Bayern Munich ba za su sake tsawaita zaman ɗan wasan Senegal Nicolas Jackson da ke zaman ɗan wasan aro a ƙƙungiyar da ga Chelsea ba a ƙarshen kakar nan ba.

    Barcelona na duba yiwuwar siyo ƴan wasa daga Machester City kamar Bernardo Silva, daɗan wasan gaba na Chelsea Pedro Neto. (Mundo Deportivo - in Spanish)

    Juventus na harin mai tsaron ragar Liverpool Alissona wannan kaka, wanda ke cikin ƴan wasan da ta ke baiwa fifiko a cefanen da za ta yi a bana. (Fabrizio Romano)

  7. Yamal ya gama buga wa Barcelona sauran wasannin bana, Barcelona

    Ɗan wasan tawagar Sifaniya, Lamine Yamal, ba zai buga sauran wasannin da suka rage wa Barcelona ba, amma ana sa ran zai murmure kafin a fara gasar Kofin Duniya.

    Matashin mai shekara 18 ya samu rauni a ƙafarsa ta hagu a lokacin da Barcelona ta doke Celta Vigo da ci 1–0 a ranar Laraba a gasar La Liga.

    Shi ne ya ci wa Barcelona ƙwallon farko daga bugun fenariti a minti na 40, amma nan da nan ya nuna alamar ya ji rauni da ya bukaci a canja shi daga karawar.

    Ƙungiyar ta tabbatar da raunin a ranar Alhamis, inda ta bayyana cewa Yamal zai ji jinya, amma ba sai an yi masa tiyata ba, kuma ba zai buga sauran wasannin da suka rage ba, duk da cewa ana sa ran zai murmure kafin gasar cin Kofin Duniya.

    Barcelona, tana kan gaba a teburin gasar da tazarar maki tara tsakaninta da abokiyar hamayyarta Real Madrid, wadda za ta fuskanta ranar 10 ga watan Mayu a cikin wasanni shida da suka rage.

    Ƙasar Sifaniya za ta fara wasanninta na Kofin Duniya a rukunin da ya haɗa da Cape Verde ranar 15 ga Yuni, sannan ta kara da Saudi Arabia ranar 21 ga watan Yuni, kafin ta haɗu da Uruguay ranar 27 ga watan Yuni.

  8. Manchester City ta ɗare kan teburin Premier League, Premier League

    Manchester City na ci gaba da matsa lamba wajen lashe gasar Firimiya ta bana, bayan da ta doke Burnley 1-0 a filin Turf Moor, wanda ya sa ta koma saman teburi, yayin da Burnley kuma za ta koma gasar Championship baɗi.

    Ƙungiyar da Pep Guardiola ke jan ragama, ta karɓe gurbin daga Gunners wacce a baya ta bayar da tazarar maki tara,

    Kafin wannan wasan City ba ta hau kan teburi ba tun fara kakar nan, amma wasa 11 da ta buga ba tare da rashin nasara ba ya sa ta samu wannan ci gaban, kuma saura karawa biyar-biyar a kammala kakar nan.

    Erling Haaland ne ya fara ci wa City ƙwallon tun farko-farkon take leda.

  9. Serhiy Rebrov ya yi Murabus daga horar da tawagar ƙwallon kafa ta Ukraine, Gasar kofin duniya

    Kocin tawagar ƙwallon ƙafa ta Ukraine, Serhiy Rebrov, ya yi murabus daga mukaminsa, kamar yadda Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Ukraine (UAF) ta sanar a ranar Laraba.

    Tsohon ɗan wasan Dynamo Kyiv da Tottenham ya karɓi ragamar horaswa a shekarar 2023, inda ya jagoranci Ukraine zuwa gasar European Championship da aka gudanar a Jamus.

    Sai dai tawagar ta kasa samun gurbin shiga gasar Kofin Duniya ta bana, bayan shan kashi da ci 3–1 a hannun Sweden a wasan cike gurbi.

    A cikin wata sanarwa, UAF ta ce Rebrov zai ci gaba da aiki da hukumar Amma a wani sabon matsayi daban.

  10. Raunin Estevao ya jefa shakkar halartarsa a kofin duniya da Brazil, Gasar Kofin Duniya

    Damar ɗan wasan Chelsea, Estevao, na wakiltar Brazil a gasar Kofin Duniya ta shiga shakku, sakamakon raunin da ya ji, wanda zai jinya zuwa karshen kakar bana.

    Mai shekara 18 ya ji rauni ne a wasan da Chelsea ta yi rashin nasara da ci 1–0 a hannun Manchester United a Premier League a Stamford Bridge ranar Asabar.

    Bayan da likitoci suka auna girman raunin da ya ji, sun sanar cewa matashi, Estavao, ya gama buga sauran wasannin Chelsea da suka rage.

    Sai dai wannan rauni ya ƙara jefa tantamar ko zai samu damar shiga cikin tawagar Brazil a gasar Kofin Duniya da za a buga a shekarar nan.

    Haka kuma Estevao na daga cikin ƴan wasan da koci, Carlo Ancelotti ke yawan amfani da shi a shirye-shiryen tawagar kafin gasar.

    Ko da yake majiyoyi kusa da Estevao sun shaida wa BBC Sport cewa ana sa ran zai murmure ya kuma kasance cikin koshin lafiyar da zai ba shi damar buga gasar, har yanzu ba a tabbatar ko Ancelotti zai yi kasadar zaɓarsa ba, musamman idan bai samu damar nuna cikakkiyar lafiya ba kafin fara wasannin rukuni ba.

    An ga Estevao cikin matsanancin damuwa yayin da yake barin fili a wasan da Chelsea ta yi da Manchester United, abin da ya nuna girman raunin da kuma tasirin da labarin ya yi masa.

  11. Chelsea ta sallami Rosenior bayan rashin nasara biyar a jere a Premier, Chelsea

    Chelsea ta sallami Liam Rosenior bayan rashin nasara biyar a jere a Premier League, kuma ta kasa zura ƙwallo a raga a cikin wasannin.

    Tsohon kocin Hull City da Strasbourg ya sanya hannu kan kwantiragin shekaru shida da rabi a watan Janairu, inda ya fara aikin da kafar dama. Sai dai daga bisani ƙungiyar ta ci karo da koma baya sosai.

    A wannan lokacin sai Chelsea ta yi da gaske sannan ta samu gurbin shiga Champions League a baɗi

    A ranar Talata, Chelsea ta sha kashi mafi muni a bana, bayan da Brighton ta doke ta 3–0 a filin Amex, wasan da masana da dama suka bayyana a matsayin mafi rauni ƙungiyar ta buga a wannan kakar.

    Biyo bayan sallamar Rosenior, Callum McFarlane ne zai karɓi ragamar horaswa a matsayin rikon ƙwarya har zuwa ƙarshen kakar wasana nan.

    Zai fara aiki ne a wasan daf da ƙarshe a FA Cup da Chelsea za ta fafata da Leeds United a ranar Lahadi.

  12. Man United za ta ɗauki Tchouaméni daga Real Madrid, Manchester United

    Ɗan wasan Real Madrid, Aurélien Tchouaméni yana cikin ƴan wasan da Manchester United ke sanya ido a shirin da take na magance matsalar masu buga mata tsakiya a kaka mai zuwa.

    Bayan da United ta yi ta fama da matsala a gurbin mai tsare raga da masu cin ƙwallo, yanzu gurbin masu buga tsakiya take son magancewa.

    Daga cikin ƴan wasan da ake alakantawa da United za ta tuntuɓa har da Elliot Anderson na Nottingham Forest da Carlos Baleba na Brighton da kuma Adam Wharton na Crystal Palace.

    Waɗannan ƴan wasan suna da kwarewa a Firimiya, hakan zai taimakawa United wajen samun abinda take bukata, kamar yadda ta samu a wajen Matheus Cunha daga Wolverhampton da Bryan Mbeumo daga Brentford.

    Rahotanni sun nuna cewa Manchester United ba wai ƴan wasan Ingila kaɗai za ta yi zawarci ba daga ciki har da Tchouaméni daga Real Madrid, wanda za ta fi mayar da hankali a kai..

    Ɗan wasan Faransa mai shekaru 26 na da kwantiragi da Real Madrid har zuwa shekarar 2028, kuma ana cewa ƙungiyar ta Sifaniya na sha’awar tsawaita yarjejeniyarsa.

    Manchester United ta nuna sha’awar ɗaukar ɗan wasan tun shekarar 2022 lokacin da ya bar Monaco, amma Tchouaméni ya zaɓi komawa Real Madrid. Tun daga wancan lokaci, ya zama ɗaya daga cikin fitattun ƴan wasan tsakiyar a duniya.

  13. Hudson-Odai ya gama buga wa Forest wasannin kakar nan, Premier League

    Callum Hudson-Odai ya gama buga wa Nottingham Forest tamaula a bana, bayan da aka yi masa tiyata kan raunin da ya ji.

    Maishekara 25 ya ji raunin a karawar da Forest ta yi nasara a Porto a zagayen kwata fainal ranar Alhamis, wanda bai buga gasar Premier da Burnley .

    Forest ta tabbatar da cewar an yi wa tsohon ɗan wasan Chelsea cikin nasara, kuma sai a cikin karshen kakar nan ake sa ran zai murmure.

    Ƙungiyar da Vitor Pereira ke jan ragama tana da tazarar maki biyar tsakani da ƴan ukun karshen teburi, kuma za ta fafata da Sunderland da Chelsea da NewcastleUnited da Manchester United da kuma Bournemouth a sauran karawa biyar da ke gabanat.

    Haka kuma za ta fafata da Aston Villa a zagayen daf da karshe a Europa League a wasan farko ranar 30 ga watan Afirilu.

  14. Dos Santos na Metz ya saka hannun kan kwantiragi bayan haɗarin gobara, Metz

    Ɗan wasan Metz, Tahirys dos Santos, wanda ya tsallake haɗarin mummunan gobara a wani gidan rawa Switzerland a daren sabuwar shekara da ta yi sanadin mutuwar mutane 41, ya saka hannun kan yarjejeniya a matakin ƙwararren ɗan ƙwallo.

    Mai shekara 19, wanda ya taka rawa wajen ceto budurwarsa a gobarar da ta tashi Le Constellation da ke wurin yawon buɗe ido a dusar kankara a Crans‑Montana, na daga cikin fiye da mutum 100 da suka jikkata a gobarar.

    Ya kone kusan kashi 30 cikin 100 na jikinsa, lamarin da ya tilasta aka yi masa dashen fata (skin graft) a asibiti.

    Bayan dogon jinya da murmurewa, Dos Santos ya koma fili a ranar 11 ga Afrilu, inda ya buga wa karamar ƙungiyar Metz wasa karon farko tun bayan hatsarin.

    Dos Santos, wanda ya shiga makarantar horaswar ta Metz tun yana da shekara takwas, yanzu ya rattaba hannu kan kwantiragin shekara guda da ƙungiyar.

    A halin da ake ciki, Metz na fuskantar mawuyacin hali a gasar Ligue 1, inda take kasa a teburin lig bayan samun nasara uku kacal daga wasanni 30.

    Kungiyar na da tazarar maki 10 tsakaninta da tsira daga faduwa, kuma saura wasa huɗu a kammala wasannin bana.

  15. Djabi na Midtjylland na cikin koshin lafiya bayan da aka Caka masa wuka a Denmark, Denmark

    Ɗan wasan Midtjylland, Alamara Djabi, na cikin koshin lafiya a asibiti bayan da ya samu munanan raunuka sakamakon wani harin da aka caka masa wuka a Denmark.

    Ƴansandan yankin sun tabbatar da cewa lamarin ya faru ne da sassafe ranar Lahadi a garin Herning, birnin da ƙungiyar Midtjylland ke da tushe.

    Djabi, mai shekaru 19 dan asalin Guinea-Bissau, ya koma Midtjylland ne a shekarar 2023 daga makarantar horaswa da ƴan wasa ta Benfica, kuma ya riga ya buga wasa biyu a babbar ƙungiyar.

    Kungiyar Midtjylland ta sana cewa ɗan wasan ya kasance “a mawuyacin hali” bayan harin, inda aka yi masa tiyata ta gaggawa domin ceto rayuwarsa.

    A kakar da ta gabata, Djabi ya buga wasa bakwai a matsayin aro tare da ƙungiyar CD Mafra a rukunin lik na biyu a Portugal. A wannan kakar kuma, ya buga wasa daya da Midtjylland a matakin tantancewa a gasar Europa League.

    Midtjylland, wadda ta lashe kofin Danish Superliga sau hudu kuma na karshe da ta ɗauka a 2024, a halin yanzu tana matsayi na biyu a teburin lig, maki biyu kacal a bayan AGF.

  16. Ƙungiyoyin Championship sun ƙi amincewa a fara mafani da VAR a baɗi, Championship

    Ƙungiyoyin da ke buga Championship gasa mai daraja ta biyu a Ingila, sun kada kuri’a ƙin amincewa da a fara amfani da fasahar da ke taimakawa alkalin wasa yanke hukunci wato VAR a baɗi.

    Tsarin da aka yi wa lakabi da Football Video Support (FVS) – wani salo ne na VAR da ke amfani da na'urar abinda ya faru ya yin wasa da ake bai wa kowane koci damar neman bitar hukunci har karo biyu a kowace wasa – ana sa ran a iya fara amfani da shi daga watan Agusta. Sai dai kungiyoyin Championship suka yi watsi da shirin.

    Hukumar alƙalan gasar ƙwararru, PGMO, ta gabatar da bayani kan tsarin FVS a taron shekara-shekara na EFL a watan da ya gabata.

    Bayan haka, EFL ta nemi ra’ayoyin ƙungiyoyi, amma yawancin ƙungiyoyin suna adawa da duk wani nau’i na tsarin nazarin bidiyo a gasar Championship.

    A halin yanzu, ana amfani da VAR a gasa mai daraja ta biyu a ƙasashen Spain da Italiya da Jamus. Haka kuma, ana shirin shigo da tsarin a Ligue 2 ta Faransa, amma shirin ya rushe ne bayan durƙushewar yarjejeniyar haƙƙin nuna wasannin a talabijin, sakamakon matsalolin kuɗi.

  17. Casemiro: Man United na cikin manyan ƙungiyoyi uku a duniya, Manchester United

    Ɗan wasan Manchester United, Casemiro, ya bayyana kaunarsa ga United, yayin da kwantiraginsa zai karea karshen kakar nan.

    Ɗan wasan Brazil mai shekaru 34 ya buga wasa a Real Madrid a shekarar 2022 daga nan ya koma United kan kuɗin fam miliyan 60, tare da rattaba hannu kan kwantaragin shekaru huɗu da zaɓin ƙarin shekara guda.

    Casemiro ya taka muhimmiyar rawa wajen kai United zuwa matsayi na uku a teburin Firimiya ƙarƙashin koci Michael Carrick. Sai dai tun daga wasa biyu karkashin Carrick aka tabbatar da cewa Casemiro zai bar ƙungiyar a ƙarshen wannan kakar.

    Tun bayan komawarsa United, Casemiro ya zura kwallaye 25 a cikin wasa 157 da ya buga. Zai sake buga wasa biyar kafin ya yi ban kwana da ƙungiyarOld Trafford.

    United tana ta ukun teburin Premier League da tazarar maki 10 tsakaninta da Chelsea ta shida, kuma saura wasa biyar-biyar a kare kakar nan.

  18. Marco Rose ya amince zama sabon kocin Bournemouth, Premier League

    Tsohon kocin Jamus, Marco Rose, ya amince da karɓar aikin horar da Bournemouth bisa kwantiragin shekara uku, wanda zai fara aiki da zarar kocin yanzu Andoni Iraola ya bar ƙungiyar a ƙarshen kakar bana.

    Bournemouth ta sanar a ranar Talata da ta gabata cewa Iraola, mai shekaru 43, ba zai sabunta kwantiraginsa ba, lamarin da ya buɗe hanyar ɗaukar wani sabon koci.

    Rahotanni sun nuna cewa Rose na daga cikin ƴan takara uku da Bournemouth ta duba kafin yanke hukunci, tare da kocin Ipswich Town, Kieran McKenna da kuma kocin Rayo, Vallecano Inigo Perez.

    Rose, mai shekaru 49, bai da ƙungiya tun bayan sallamarsa daga RB Leipzig a watan Maris a shekarar 2025, kuma wannan ne karon farko da zai yi aikin horaswa a kasar Ingila.

    Ya fara aikin kociya tun a shekarar 2012 da Lokomotive Leipzig, sannan ya rike shugabanci a manyan ƙungiyoyi da suka haɗa da Red Bull Salzburg da Borussia Dortmund da Borussia Monchengladbach da kuma RB Leipzig.

    A nasarorin da ya samu, Rose ya jagoranci Red Bull Salzburg zuwa lashe gasar Austrian Bundesliga biyu tare da kofin Austrian Cup, sannan ya lashe DFB-Pokal da kuma DFL-Supercup yayin da yake tare da RB Leipzig.

  19. Lukaku zai ci gaba da jinya a Belgium bayan tattaunawa da Napoli, Serie A

    Ɗan wasan Napoli, Romelu Lukaku, zai ci gaba da jinya a ƙasar Belgium bayan ganawa da samun maslahah da shugabannin ƙungiyar suka yi a birnin Naples.

    A watan Maris, rahoton BBC ya bayyana cewa tsohon ɗan wasan Manchester United da Chelsea da Everton na fuskantar yiwuwar ladabtarwa daga Napoli, bayan zargin ya yi watsi da umarnin komawa horo a Italiya.

    Kakar wasannin Lukaku ta samu cikas sakamakon raunin da ya ji, wanda ya takaita wasanninsa zuwa bakwai kacal. Wasan karshe da ya buga shi ne shiga canji a wasan da Napoli ta doke Torino 2–1 a ranar 6 ga watan Maris.

    Tun daga nan, ɗan wasan mai shekaru 32 ya koma ƙasarsa ta Belgium, sakamakon jin rauni lamarin da ya sa ya kasance nesa da cibiyar atisayen Napoli.

    Sai dai daga baya Lukaku ya koma Naples domin tattaunawa da ƙungiyar, ganawar da aka bayyana a matsayin “fuskantar juna, haɗin kai da amfani ga ɓangarorin biyu.” Taron ya samu halartar wakilinsa, Federico Pastorello, da daraktan wasanni na Napoli, Giovanni Manna.

    Rahotanni sun nuna cewa tattaunawar ta kai ga fahimtar juna tsakanin ɓangarorin, inda majiyoyi suka tabbatar da cewa an rufe batun gaba ɗaya cikin kwanciyar hankali.

    A yayin tattaunawar, Lukaku ya yi wa Napoli bayani kan yadda jinyarsa ke tafiya. Ana sa ran ɗan wasan zai kasance cikin shirin dawowa buga wasanni nan da kimanin makonni biyu masu zuwa.

  20. Haaland Ya Soki Arsenal, Ya Ce Sun Sha Gazawa a Lokutan Baya, Premier League

    Tauraron ɗan wasan Manchester City, Erling Haaland, ya yi wa Arsenal tuni da irin gazawar da suka yi a kakar wasanni da ta gabata da Liverpool ta lashe Premier League, bayan da ya taimaka wa kungiyarsa wajen samun muhimmiyar nasara a kan abokan hamayyarta na neman kofin Firimiya.

    Dan wasan Norway ya ci kwallon na biyu da Manchester City ta doke Arsenal 2–1 a filin Etihad ranar Lahadi, hakan ya sa saura maki uku tsakanin Arsenal ta daya da kuma City ta biyu a teburin Premier League.

    City na da kwantan wasa, kenan tana da damar hayewa kan teburin babbar gasar tamaula ta Ingila daga nan zai rage wasa biyar-biyar a kammala kakar bana.

    Haaland ya amince cewa Arsenal ce ta fi nuna bajinta a yawancin kakar wasan nan, amma ya kara da cewa Manchester City ba za ta ja da baya ba wajen kalubalantarsu, domin hana su lashe kofin gasar Firimiya da rabon Arsenal da shi 2004.

    “Mun san Arsenal kungiya ce mai karfi, amma mun ga a baya sun taba zuwa kusa ba tare da sun kai ga buri ba,” in ji Haaland bayan wasan.