Iran ta sake kai sabbin hare-hare a Kuwait da Jordan
Iran ta ci gaba da kai hare-hare kan wurare daban-daban a yankin gabas ta tsakiya, bayan sojojin Amurka sun bayyana cewa sun kai jerin hare-haren sama da suka kai kan Iran cikin daren jiya.
Kuwait ta ce wani makami mai linzami da Iran ta harba ya faɗa kan wani gini a arewacin ƙasar, inda ya kashe mutum ɗaya.
Sojojin Jordan kuwa sun ce sun harbo makamai masu linzami guda biyar da Iran ta harba.
Tun da farko, sojojin Amurka sun ce sun kai hari kan wurare da dama mallakin rundunar Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC) ta Iran, a matsayin martani ga harin makamai masu linzami da Iran ta kai ranar Talata kan wani sansanin sojojin Amurka da ke Jordan.
Kafofin yaɗa labarai na Iran sun ce hare-haren na baya-bayan nan da Amurka ta kai sun kashe mutane uku, ciki har da wani yaro.