Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 01/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan yaƙin Iran da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 01/06/2026.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, A'isha Babangida, Haruna Kakangi

  1. Zanga-zanga ta ɓarke a Oyo kan sace ɗaliban jihar

    Ɗaruruwan malaman makaranta da iyaye da ƙungiyoyin matasa sun fantsama titunan jihar Oyo domin yin zanga-zanga kan abin da suka kira rashin taɓuka komai daga gwamnati don ceto ɗalibai da wasu malamansu da ƴanbindiga suka sace makwanni biyu da suka gabata.

    Masu zanga-zangar ɗauke da alluna da ƙaton allo ɗauke da hotunan yara, wasu cikin tsoro wasu kuma na nuna jikinsu da tabbai.

    Wasu yara ƴan shekara 12 zuwa 15 suma sun bi sahun masu zanga-zangar.

    Zanga-zangar wani ɓangare ne na matakan malaman makarantun gwamnati karƙashin ƙungiyar malamai ta NUT na matsa wa gwamnati lamba ta kuɓutar da ɗalibai da malamansu da aka sace a watan da ya gabata.

  2. Gagarumar fashewa ta halaka mutum kusan 50 a Myanmar

    Aƙalla mutum 46 aka kashe, wasu da dama kuma suka ji rauni bayan wata fashewa a wani ƙauyen yankin Myanmar da ke hannun ƴanbindiga.

    Tawagar masu aikin ceto sun shaida wa BBC cewa daga cikin mamatan har da ƙananan yara shida har da wani ɗan shekara ɗaya.

    Fashewar ta lalata kusan gidaje 200 a Kaung Tat da wasu 100 da ke ƙauyen Pan Lone mai maƙwabtaka.

    Mayaƙa TNLA da ke riƙe da yankin kuma take yaƙi da gwamnatin soji ta ce abubuan fashewar da aka ajiye ne suka tashi, lamarin da ya janyo fashewar.

  3. DSS ta kama mutum biyar kan zargin hannu a sace ɗaliban Papiri

    Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya DSS ta kama mutum biyar ciki har da ƴan Nijar biyu da ake zargin suna kai wa ƴanbindiga makamai waɗanda a ranar 21 ga Nuwambar bara suka kai hari kan wata makaranta a ƙauyen Papiri da ke jihar Neja, inda suka sace ɗalibai kusan 300 da malamai.

    Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa daga cikin makaman da aka samu a hannun mutanen akwai tarin bindigogi da alburusai.

    Wasu majiyoyi da Channels ta ruwaito cewa Yusuf Mohammed da aka fi sani da Bature, wanda sunansa ke cikin jerin mambobin Boko Haram da ake ema ruwa a jallo sai Mubarak Ibrahim da aka kama a kan babbar hanyar Zaria zuwa Kaduna yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa karɓar ƙunshin makamai da za su kai wa kwamandojinsu.

    Majiyar ta kuma ce wani samame da aka kai ya sa an kama Goni Ibrahim, da ya yi ƙaurin suna wajen safarar makamai daga Diffa a Jamhuriyar Nijar. Baya ga shi, an kuma kama Tukur Sani wanda suke aikin tare.

  4. Ana zanga-zanga a Kenya kan shirin buɗe cibiyar Ebola ta Amurka a ƙasar

    Zanga-zanga ta ɓarke a garin Nanyuki da ke Kenya game da shirin gina cibiyar killace masu Ebola ta Amurka a sansanin sojin sama na Laikipia.

    Mazauna garin sun yi tattaki inda suke ihu, wasu kuma sun toshe tituna lamarin da ya sa ƴansanda suka harba hayaƙi mai sa hawaye domin tarwatsa masu zanga-zangar.

    A cewar masu zanga-zangar, cibiyar na iya jefa rayukan mutanen ganin cikin haɗari da kuma yiwuwar ɓarkewar cutar.

    Joyce Wangui, wata mazauniyar Nanyuki ta ce "abin takaici ne yadda gwamnati ta nuna rashin damuwarta game da lafiyar ƴaƴanmu da al'ummarmu. Ba ma son a gina wannan cibiya a Laikipia."

    Marlin Ndegwa, wani shugaban al'ummar yankin ya ce masu zanga-zangar sun ɗauki matakin ne domin su nuna rashin goyon bayansu ga gina cibiyar Ebola a garin.

    A makon da ya gabata ne wata kotun Kenya ta dakatar da shirin Amurka na buɗe cibiyar killace masu Ebola ta Amurkawa a ƙasar. Lamarin dai ya janyo cece-kuce da kuma damuwa a tsakanin jama'a.

    Zuwa yanzu ba a samu ɓullar Ebola a Kenya ba sai dai ma'aikatar lafiya ta kafa cibiyar kula da kuma killace masu cutar a sassan ƙasar.

  5. Ƴansanda sun yi gargaɗi game da harin martani kan ƴan Afirka ta Kudu

    Ƴansanda a Najeriya sun yi gargaɗi kan kai hare-haren ramuwar gayya kan ƴan Afirka ta Kudu ko ma wuraren kasuwancinsu sakamakon zanga-zangar ƙin jinin baƙi da ake yi a Afirka ta Kudun.

    Ƴansanda sun buƙaci ƴan Najeriya da kada su ɗauki doka a hannunsu bayan "rahotannin hare-hare kan ƴan Najeriya a Afirka ta Kudu".

    Ba a samu rahoton faruwar irin hare-haren ba amma gargaɗin na zuwa ne bayan wani taron manyan jami'an tsaro.

    Ƴansandan Afirka ta Kudu ba su tabbatar da hare-hare kan baƙi ba duk da cewa gwamnati ta yi allawaai da miyagun laifukan da ake aikatawa kan baƙi.

    A baya-bayan nan ana ta zaman ɗar-ɗar a Afirka ta Kudu sakamakon zanga-zangar neman a tsaurara matakai kan baƙin haure.

    Ƙasashen Afirka da dama sun shawarci al'umominsu da su kasance cikin shirin ko ta kwana, inda a baya-bayan nan Ghana ta kwashe ɗaruruwan ƴan ƙasarta saboda tabbatar da tsaronsu.

  6. An haramta wa ƴara buɗe shafukan sada zumunta a Malaysia

    Malaysia ta fara hana ƴan ƙasa da shekara 16 daga buɗe shafukan sada zumunta.

    Hukumar kula da harkokin sadarwa ta ƙasar ta ce dole ne shafuka kamar Fesbuk da Instagram da Tikok da YouTube su tantance shekaru kan bayanan gwamnati da aka bayar.

    Malaysia ta bi sahun ƙasashen da suka bijiro da matakai makamancin haka domin kare yara daga ganin abubuwan da ba su kamata ba a shafukan sada zumunta.

    Kamfanonin da suka gaza martaba matakin zai fuskanci tarar kusan dala miliyan biyu da rabi.

  7. Malamai sun shiga yajin aiki kan sace ɗaliban Oyo

    Ƙungiyar malamai ta Najeriya ta umarci malama makarantun firamare da sakandare a jihar Oyo su shiga yajin aiki daga yau Litinin har sai abin da hali ya yi.

    Umarnin ya fito daga shugabancin ƙungiyar na ƙasa a matsayin nuna damuwa kan ci gaba da tsare malamai da kuma ɗaliban da aka sace, wanda zuwa yanzu ba a da tabbaci kan lokacin da za a kuɓutar da su ba.

    A cewar ƙungiyar, ci gaba da tsare ɗaliban da malaman na ƙara haifar da fargaba a tsakanin malamai tare da sa iyaye yin baya-baya da tura ƴaƴansu zuwa makaranta.

    Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa lamarin ya zo ne bayan umarnin da Shugaba Bola Tinubu ya bayar a ranar Lahadi na ɗaukan jami'an tsaron gandun daji 1,000 domin taimakawa wajen kuɓuto da malamai da ɗaliban da aka sace.

    A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar reshen Oyo Kwamared Hassan Fatai ya sanyawa hannu, NUT ta ce an ɗauki matakin domin jawo hankalin hukumomi su gaggauta ruɓanya ƙoƙarinsu na ganin an sako waɗanda akae garkuwa da su ba tare da ɓata lokaci ba.

  8. Amurka ta kai 'hare-haren martani' kan Iran

    Sojojin Amurka sun ce sun kai hare-hare kan wuraren samar da jirage marasa matuƙa na Iran a birnin Goruk da kuma tsibirin Qeshm a ƙarshen mako.

    Rundunar sojin Amurka a gabas ta tsakiya ta bayyana a shafinta na sada zumunta cewa an kai hare-haren ne a matsayin martani ga abin da ta kira “Matakan tsokana daga Iran”, waɗanda suka haɗa da harbo wani jirgin leƙen asiri marar matuƙi na Amurka, wanda take ikirarin yana shawagi ne a sararin samaniyarta.

    A matsayin martani, dakarun juyin juya halin Musulunci na Iran sun ce sun kai hari kan wani sansani da sojojin Amurka ke amfani da shi, sai dai ba su bayyana sunan sansanin ba.

    Tun da fari, Kuwait ta ce ta dana garakuwar tsaron sararin samaniyarta, don harbo wani makami mai alinzamia da Iran din ta harba.

  9. Mutum huɗu sun warke daga cutar Ebola

    Hukumomin lafiya a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo sun yi murnar warkewar mutum huɗu da suka tsira daga cutar Ebola.

    Suna daga cikin mutanen farko da aka sallama daga cibiyoyin jinya tun bayan barkewar cutar da aka samu a yanzu.

    A wani biki da aka gudanar a Bunia, wanda shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya halarta, an yaba wa mutanen da suka warke wadanda dukkaninsu ma’aikatan lafiya ne bisa jarumtar da suka nuna.

    Mutanen sun kamu da Ebolar ne yayin da suke kula da masu cutar, kuma sun ce sun ji dadi kwarai-kwarai da suka samu lafiya.

  10. Barkan mu da warhaka!

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye na ranar Litinin 1 ga watan Yuni 2026.

    Wannan shafi zai kawo muku duk muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya tsokaci kan abubuwan da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta: facebook, X, Instagram da kuma YouTube.