Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Alhamis 14//05/2026

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, da Usman Minjibir da Aisha Babangida

  1. An zaƙulo matattu daga ɓuraguzai a Kyiv

    Jami'ai a Kyiv sun ce an zaƙulo gawawwakin mutum uku daga ɓuraguzan ginin da Rasha ta kai wa hari a Kyiv inda ake ci gaba da aikin ceto sakamakon ɓarnar da hare-haren suka yi.

    Aƙalla mutum 144 ne suka ji rauni har da yara biyu, in ji magajin garin. 21 cikinsu suna samun kulawa a asibiti, har da yaro guda.

    Rana ta uku ne nan da Ukraine ke bayar da rahoton mace-mace yayin da Rasha ke zafafa hare-hare bayan da yarjejenyar tsagaita wuta ta ƙare ranar Litinin.

    A hare-haren na cikin dare, an harba fiye da jirage marasa matuƙa 670 sai makamai masu linzami 56 zuwa sassan Ukraine, kamar yadda Shugaba Volodomyr Zelensky ya bayyana.

  2. 'Amurka da China sun haɗu kan manufar hana Iran mallakar makamin nukiliya'

    Fadar White House ta ce Shugaba Trump da takwaransa na China, Xi - da ke ganawa a Beijing - sun amince cewa bai kamata Iran ta mallaki makamin nukiliya ba kuma ya zama dole a buɗe Mashigar Hormuz.

    Wata sanarwa daga Amurka game da ganawar ta tsawon sa'a biyu ta ce akwai fahimtar juna tsakaninsu kuma shugabannin biyu suna aiki don inganta alaƙarsu ta tattalin arziki sai dai sanarwar ba ta ambaci ɗaya daga cikin batutuwan da suke taƙaddama a kai ba - Taiwan.

    Mista Xi ya ce ya kamata Amurka da China su zama "abokan hulɗa ba abokan gaba ba" sai dai ya yi gargaɗin za a iya samun saɓani kan maganar Taiwan.

  3. NEMA ta buƙaci jihohi su ɗauki matakan kariya daga ambaliya

    Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya ta yi kira ga gwamnonin jihohi da u fara ɗaukan matakan riigakafi da nufin kaucewa matsalar ambaliya sakamakon hasashen da aka yi cewa fiye da jihohi 30 na iya fuskantar gagarumar matsalar ambaliya a daminar bana.

    A cewar saƙon da NEMA ta wallafa a shafinta na X, Shugabar hukumar Zubaida Umar ta yi kira ga jihohin da su gaggauta ɗaukan mataki domin rage tasirin ambaliyar da aka yi hasashen za a samu a wasu yankunan ƙasar.

    Sanarwar ta ce wasu daga cikin matakan da ake tsammanin jihohin su ɗauka sun haɗa da sake farfaɗo da shirin tsaftar muhalli duk wata da yawan gyara magudanan ruwa da hanyoyin wucewar ruwa.

    Shugabar NEMA ta kuma ce yi kira ga sarakunan gargajiya da malaman addini da ƙungiyoyin matasa da kafafen yaɗa labarai da kamfanoni masu zaman kansu da su tallafa wa ƙoƙarin hukumar wajen kare afkuwar ambaliya a ƙasar

  4. ‘Netanyahu bai ziyarci Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa a asirce ba’

    Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta musanta cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya kai wata ziyarar sirri ƙasar, duk da cewa ofishin Mista Netanyahu ya sanar da ziyarar ne sa'o'i kaɗan kafin hakan.

    Wakiliyar BBC ta ce Ma'aikatar harkokin wajen haɗaɗɗiyar daular larabawar ta musanta batun ziyarar da kakkausar murya inda ta ce dangantaka da Isra'ila a fili ake gudanar da ita kuma duk wani iƙirari game da ziyarar da ba a sanar ba "ba ta da tushe.

    Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta kasance ɗaya daga cikin ƙasashen Larabawa da dama da suka ƙulla hulɗar jakadanci da Isra'ila bayan yarjejeniyar Abraham Accords a wa'adin shugabancin Trump na farko.

  5. Ana laluben mutanen da suka mutu bayan harin Rasha a Kyiv

    Magajin garin Kyiv ya ce Rasha ta kai wani gagarumin hari ta sama kan babban birnin na Ukraine kuma tuni jami'ai suka duƙufa domin duba ɓuraguzai don zaƙulo waɗanda lamarin ya rutsa da su.

    Lamarin ya yi ajalin mutum biyu sai wasu 40 da suka ji rauni kamar yadda jami'ai suka bayyana.

    Vitaliy Klitschko, wanda ya ziyarci ginin da lamarin ya shafa, ya ce lamarin ya shafi ɗakuna 18.

    A cewar shi, harin ya lalata hanyoyin samar da ruwa na birnin.

    A ranar Laraba Rasha ta kai hari mafi girma da aka kai ta sama kan Ukraine tun bayan fara yaƙi tsakanin ƙasashen.

    Shugaba Zelensky ya ce Moscow ta harba wasu jiragen sama marasa matuƙa sama da ɗari takwas kuma tuni aka kuɓutar da mutane gommai daga ginin.

  6. Ministan harkokin wajen Iran ya halarci taron BRICS a Indiya

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya isa ƙasar Indiya domin halartar taron ministocin harkokin wajen ƙasashen BRICS.

    Yayin wannan ziyara, ana sa ran Mista Araghchi zai gana tare da tattaunawa da takwarorinsa daga sauran ƙasashe yayin da yake halartar taron.

    Rahotanni sun ce yaƙin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran shi ne babban abin da ke jan hankali a tattaunawar da mambobin ƙungiyar ke yi.

    Ana gudanar da taron ministocin harkokin wajen BRICS na kwanaki biyu ne a birnin New Delhi na ƙasar Indiya.

    BRICS ƙungiya ce da ta ƙunshi manyan ƙasashe masu tasowa a duniya. Brazil da Rasha da Indiya da China da kuma Afirka ta Kudu su ne manyan mambobin ƙungiyar. Sunan BRICS ya samo asali ne daga haruffan farko na sunayen ƙasashen a harshen Igilishi.

    Iran ta zama cikakkiyar mamba a ƙungiyar shekaru biyu da suka gabata.

  7. Jami'an kwastam biyu sun mutu a fafatawa da Lakurawa

    Jami'an hukumar kwastam biyu sun rasa ransu a fafatawar da suka yi da mayaƙan da ake zargi Lakurawa ne a jihar Kebbi.

    Shugaban hukumar kwastam, Bashir Adeniyi, ya ce lamarin ya faru ne da safiyar ranar Laraba.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa jami'an masu muƙamin ASC da DSC, sun rasa ransu ne yayin samamen yaƙi da ƴan ta'adda da tsakiyar dare.

    Adeniyi ya faɗi hakan ne a birnin Illorin yayin da yake gabatar da jawabi a jami'ar Illorin da ke jihar Kwara.

    Rahotanni sun ce maharan sun farwa shingen binciken ababen hawa na tsaro da ke kusa da juna.

    A nan ne kuma suka harbi jami'i guda sannan suka cinna wa ɗaya jami'in wuta da ransa.

    Gwamnan jihar Kwara, AbdurRahman AbdulRazaq ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga hukumar ta kwastam kan mutuwar jami'an biyu inda ya bayyana su a matsayin ƴan kishin ƙasa da suka rasa ransu yayin hidimta wa ƙasarsu.

  8. Indiya ta gargaɗi duniya kan rikice-rikicen da ke girgiza tattalin arziki

    Ministocin harkokin wajen ƙasashen BRICS ciki har da Iran da Rasha sun gana a birnin New Delhi na ƙasar Indiya, inda gwamnatin Indiya ta bayyana damuwa kan yadda rikice-rikice ke ƙara jefa duniya cikin rashin tabbas a tattalin arziki da harkokin makamashi.

    Yaƙin Iran da matsalar man fetur da ta biyo baya sun mamaye muhawarar taron na kwanaki biyu.

    A jawabin buɗe taron, ministan harkokin wajen Indiya, Subrahmanyam Jaishankar, ya ce duniya na cikin wani yanayi mai cike da sauye-sauye da tashin hankali a dangantakar ƙasa da ƙasa.

    Ya ce rikice-rikice, matsalolin tattalin arziki, ƙalubalen kasuwanci da fasaha, da kuma sauyin yanayi na ci gaba da sauya tsarin duniya.

    Jaishankar ya ƙara da cewa ƙasashe masu tasowa na sa ran BRICS za ta taimaka wajen samar da kwanciyar hankali da daidaito a duniya.

    Haka kuma ya ce ƙasashe da dama har yanzu na fuskantar matsaloli da suka haɗa da tsaron makamashi, samar da abinci da taki, harkokin lafiya da kuma samun kuɗaɗen tallafi.

  9. Ya kamata Amurka da China su zama abokan hulɗa ba na hamayya ba - Xi Jinping

    Shugaba Xi Jinping na China ya shaida wa Donald Trump cewa, kamata ya yi ƙasashensu su kasance abokan hulɗa, ba abokan hamayya ba, a farkon tattaunawar shugabannin biyu a birnin Beijing.

    Shugaba Trump ya ce a yanzu dangantakar da ke tsakanin manyan ƙasashen biyu za ta inganta fiye da kowane lokaci a tarihi.

    Ya ce abin da mutane ba su sani ba shi ne duk lokacin da aka samu matsala muna warware ta cikin sauƙi kuma za mu ci gaba da tabbatar da danƙon zumuncin da ke tsakanin mu.

    Mista Trump yana tafiya ne tare da wata babbar tawaga da ta ƙunshi manyan jami'an gwamnati da shugabannin kamfanonin fasaha da suka haɗa da Elon Musk da kuma shugaban kamfanin Nvidia Jensen Huang.

  10. Barka da Safiya

    Shafin Kai Tsaye na BBC Hausa na yi wa ɗumbin masu kasancewa da mu barka da wannan lokaci.

    Da fatan an wayi gari cikin ƙoshin lafiya. Kamar kodayaushe, a yau ma za mu ci gaba da kawo maku rahotanni na abubuwan da suka shafi yaƙin Iran da labaran da suka danganci Najeriya da sauran ƙasashen duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labarai da ma kallon bidiyo.