Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Me ya sa kwamandojin Amurka ke gargaɗi kan ci gaba da yaƙin Iran?
- Marubuci, Shaida Houshmandi
- Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC, Washington
- Aiko rahoto daga, واشنگتن
- An wallafa
- Lokacin karatu: Minti 6
A farkon watannin yakin Iran da Amurka, kafafen yaɗa labarai na Amurka sun riƙa tambayar yadda Washington za ta iya tilasta Tehran ta amince da buƙatunta, yanzu babban tambayar da suke yi kuma ta sauya: har zuwa yaushe Amurka za ta iya ci gaba da wannan yaƙi, mene ne zai faru idan aka ci gaba da shi, kuma idan ba a cimma abin da ake so ba, ta yaya za a fita daga yakin?
Jaridar The Washington Post, ta dogara da wani rahoton sirri na ma'aikatar tsaron Amurka Pentagon, kuma a kan shi ta bayar da rahoton cewa wasu daga cikin manyan kwamandojin sojojin Amurka sun gargadi Sakataren Tsaron ƙasar Pete Hegseth cewa ci gaba da yaƙi da Iran a wannan yanayin da ake ciki yanzu ba zai kasance abu mai dorewa na dogon lokaci ba.
Jaridar ta ce waɗannan kwamandoji sun yi gargadin cewa wannan yanayi na iya rage ƙarfin Amurka wajen tunkarar barazana a wasu sassan duniya, har ma da kare kasar.
An fitar da sanarwar gargadin ne a cikin rahoton wani nazari da aka yi na ranar 14 ga Agusta daga Ofishin Sakataren Tsaro, wasu bayanai da ke nazarin kan halin jiragen ruwa, jiragen sama, sojoji da tsarin makaman Amurka a faɗin duniya.
Bisa ga wannan rahoto, kwamandojin sojojin Amurka da ke Turai, da yankin Pacific da Latin Amurka, tare da Babban Kwamandan Ruwa, sun nuna adawa da ci gaba da tura kayan yakinsu zuwa Babbar Rundunar, duk da cewa a ƙarshe dole su aiwatar da umarnin Sakataren Tsaro.
Wata majiya da ta san abin da ke faruwa ta shaida wa jaridar The Washington Post cewa mafi yawan kwamandojin suna ganin yaƙin da ake yi dangane da Iran ya ɗauki lokaci mai tsawo kuma ya yi tsayi fiye da kima.
A cewar majiyoyin jaridar, Admiral Daryl Caudle, shugaban da ke kula da ayyukan rundunar ruwa, ya yi gargadin cewa rundunar ruwa ba za ta iya ci gaba da bayar da tallafin yaƙi a wannan matakin ba sai an ayyana takamaiman lokacin da yaƙin zai ƙare.
Rahoton The Washington Post ya kuma nuna irin matsin lambar da yakin ke jefa sojojin Amurka ciki. Bisa ga rahoton, kusan kashi ɗaya cikin huɗu ne kawai na jiragen ruwan yaƙi masu linzami na rundunar sojin ruwa a yanzu ke shirye don aiki nan take, adadin da ya nuna raguwa sosai idan aka kwatanta da yadda yaƙin ya fara.
Haka kuma an rage yawan makaman kariya na Patriot, makaman THAAD da makaman Tomahawk, yayin da kusan kashi ɗaya cikin huɗu na jirage marasa matuki na Reaper na Pentagon duka aka ƙarar.
Sai dai gwamnatin Trump ta ce rahotannin da ke magana kan ƙarancin makamai ko alburusai ba su da inganci.
Duk da haka, damuwar kwamandojin ba ta takaita ga adadin makamai masu linzami da jiragen ruwa kawai ba. An riga an cire sojojin da aka kawo daga Turai, Latin Amurka da yankin Pacific domin yakin Iran an tura su wasu wuraren na daban. Haka kuma da mafi yawa daga rundunonin sojojin sama da aka tura Gabas ta Tsakiya yanzu an dawo da su yankin har sai shekarar 2027.
A cewar The Washington Post, wasu kwamandojin na ganin waɗannan maye gurbin sun rage damar horar da wasu sojin, shirin ko ta kwana, da kuma aiwatar da wasu ayyuka.
A yankin Pacific, ƙawayen Amurka ma sun nuna damuwa cewa raguwar makamai a rumbunanan ajiya na rage ƙarfin barazanar da ake yi wa China. Har ma da jirgin ruwan ɗaukar jiragen sama USS George Washington, wanda ke taka muhimmiyar rawa a shirin Amurka na dakile Beijing, an mayar da shi yankin domin tallafa wa yaƙin Gabas ta Tsakiya.
Me ya sa Amurka ba za ta yi watsi da yaƙin ba?
A cikin wani hasashen masana da ya zo daidai da cika shekaru biyar da janyewar sojojin Amurka daga Afghanistan, jaridar The New York Times ta duba yaƙin Iran daga wata mahangar.
Greg Jaffe, mai rahoto kan harkokin soja na jaridar, ya fara makalarsa da cewa a mafi yawan lokacin yaƙin Afghanistan, abin da ya fi wahala ga Amurka fiye da cin nasara shi ne yadda za ta fita daga yakin.
Daga nan ya kwatanta yaƙin Afghanistan da halin da ake ciki yanzu a Iran, yana mai cewa babu wata alama bayyananniya cewa sojojinsu za su samu nasara a kan Iran, kuma Donald Trump a wasu lokuta ya ta nuna alamun son kawo ƙarshen yaƙin, amma a kowane lokaci zai yi magana sai ya sake jaddada muhimmancin ci gaba da kasancewa cikin yakin.
The New York Times ta yi tambaya ko dalilan da suka sa Amurka ta daɗe a Afghanistan na tsawon shekaru za su sake jefa ƙasar cikin wani dogon yaki da Iran.
Makalar ta ambato cewa Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya jaddada a farkon wannan yaƙin cewa wannan ba zai yi tsayi ba kamar na Iraki ko Afghanistan ba. Ya bayyana shi a matsayin yaƙi mai dogon buri, da ke gudana cikin sauri, mai cike da yaudara yana mai cewa kai tsaye: "Wannan ba yaƙi ne mara iyaka ba."
Sai dai a watannin da suka biyo baya, manufofi da burikan yakin sun fara sauyawa. Janar Dan Caine, shugaban Hafsoshin Sojojin Amurka, ya taɓa amincewa a gaban Majalisa cewa karfin hare-haren sama yana da iyaka, kuma bama-bamai kaɗai ba za su iya kayar da Iran ko bude mashigar Hormuz gaba ɗaya ga zirga-zirgar jiragen ruwa na kasuwanci ba.
A cewar The New York Times, gwamnatin yanzu tana fatan cewa hana fitar da kayayyakin Iran ta ruwa da kuma takunkumin kudi za su samar da sakamakon da hare-haren farko suka kasa samarwa.
A yanzu, batun ya fi karkata daga "neman nasara cikin gaggawa" zuwa wani shiri da zai iya ɗaukar watanni masu yawa ko ma fiye da haka. Da aka tambayi Hegseth ko rundunar ruwa za ta iya ci gaba da hana fitar da kayan Iran, sai ya ce Amurka za ta iya ci gaba da yin hakan "muddin ya zama dole", ko da kuwa har na tsawon lokaci marar iyaka.
Kwatancen da ake yi da Afghanistan a nan yana da alaƙa da lokaci. Taliban suna fafutukar rayuwarsu ne, kuma suna iya jurewa fiye da gwamnati da jama'ar Amurka. A ra'ayin marubucin, shugabannin Iran ma yanzu suna kallon batun a matsayin na rayuwa ko mutuwa, yayin da abin da Amurka ke fuskanta a wannan yaki ba barazana ce ga samuwarta a matsayin ƙasa ba.
A ƙarshe, The New York Times ta kammala da yiwuwar cewa tsadar ƙara faɗaɗa ayyukan soja domin sake bude Mashigar Hormuz gaba ɗaya, ta fuskar rayukan mutane da kuma kuɗaɗen da za a kashe, na iya zarce abin da shugaban ƙasa ko jama'ar Amurka suka shirye su amince da shi.
'Yan Republican sun yi gargadi kan ƙarewar makamai
Batun gazawar ƙarfin sojin Amurka ba ta takaita ga jaridun The Washington Post da The New York Times kaɗai ba, har ma ta bayyana a kafafen yaɗa labarai masu ra'ayin mazan jiya.
Brian Mast, shugaban Kwamitin Harkokin Waje na Majalisar Wakilai kuma ɗan jam'iyyar Republican, ya kare matakin gwamnatin Trump na ƙara matsin lamba kan Iran a shirin Sunday Morning Futures na Fox News, yana cewa abin da ake yi wa Tehran shi ne "cikakken matsin lamba." Sai dai ya yi gargadin cewa yakin na saurin rage rumbun ajiyar makamai da alburusai na Amurka, kuma hakan na iya sa ƙasar ta zama cikin haɗari lokacin fuskantar China da Rasha.
Mast bai yi kira ga gwamnatin da ta janye manufofinta ba, kuma bai ce matsin lambar da ake yi wa Iran kuskure ba ne. Amma kalamansa na nuna cewa ko a tsakanin 'yan jam'iyyar Republican mai mulki a White House, batun ƙarfin soja ya zama wani muhimmin ɓangare na lissafin da ake yi game da mataki na gaba a yakin.
Wani ɗan Republican daban ya nuna damuwar siyasa da zaɓe da Mista Brian Mast ya taɓo.
Dan majalisar wakilai na jihar Michigan, John James, wanda tsohon sojan yakin Iraki ne kuma ɗan takarar gwamnan jihar, ya bayyana a shirin Face the Nation na CBS. JIhar da ke ɗaya daga cikin jihohin da ke da muhimmanci sosai ga jam'iyyun biyu a zaɓukan da ke tafe.Mai gabatar da shirin, Margaret Brennan, ta fara tattaunawar da nuna bambanci tsakanin alkawuran farko da abin da ya faru a zahiri: rikicin ya shiga wata na shida, alhali a farko an ce zai ɗauki makonni kaɗan ne kawai. Ta kuma ƙara da cewa, bisa wani binciken ra'ayin jama'a na CBS, kashi 61 cikin 100 na Amurkawa suna adawa da yakin.
Daga nan Brennan ta yi tambayoyi biyu: Shin James ya amince da abin da yake kama da sauyin gwamnatin daga amfani da ƙarfin soja zuwa hanyoyin tattalin arziki? Kuma shin jama'ar Amurka ba su cancanci samun ƙarin bayani game da shirin da ake da shi na gaba ba?
James bai amsa tambaya ta biyu kai tsaye ba. Da farko ya ce taken "Mutuwa ga Amurka" ya kamata a ɗauke shi da muhimmanci, kuma ya goyi bayan ƙoƙarin gwamnatin na hana Iran mallakar makamin nukiliya.