Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Lahadi 24/05/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Lahadi 24/05/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Isra'ila ta ce ta lalata rumbunan ajiyar makaman Hamas uku a Gaza

    Sojojin Isra'ila sun ce sun kai hare-hare tare da lalata rumbunan ajiyar makaman Hamas a tsakiyar Gaza cikin sa'a 24.

    A cewar Isra'ilar, waɗannan rumbunan na ɗauke da tankokin harba makaman linzami da makamai masu cin dogon zango da RPG da sauran makamai.

    Cikin wata sanarwa da sojojin Isra'ila suka fitar sun ce za su ci gaba da aiki da yarjejeniyar tsagaita wuta, yayin da za su ci gaba da kawar da duk wani abu da suka kira barazana.

  2. 'Muna fatan ganin yarjejeniyar da za ta tabbatar da buɗe mashigar Hormuz'

    Firaministan Birtaniya, Sir Keir Starmer ya yi maraba da ci gaban da aka samu a tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin Iran.

    ''Muna fatan ganin yarjejeniyar da za ta tabbatar da sake buɗe mashigar Hormuz ba tare da wani sharaɗi ba'', in ji Keir Starmer.

    Firaministan ya kuma jaddada buƙatar ''hana Iran ƙera makamin nukiliya''.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, ya ce a shirye Birtaniya take ''ta yi aiki da ƙasashen duniya don hana Iran wannan dama da ta jima da buri''.

  3. China na amfani da mutum-mutumi don ceto masu haƙar ma'adinan da suka maƙale

    Ana ci gaba da aikin neman masu aikin haƙar ma'adanai da suka maƙale ƙarƙashin ƙasa a Yammacin China, inda aka tura mutum-mutumi masu na'ura a ramukan na ƙarƙashin ƙasa masu gubar iskar gas mai haɗari.

    Tun a ranar Juma'a ne, haɗarin ya auku inda kafofin yaɗa labaran ƙasar suka ce fashewar iskar gas ce ta janyo, har ta hallaka akalla mutum 82, a mahakar ta kwal, wasu ma'aikatan kuma sama da 100 aka garzaya da su asibiti.Kafafen yaɗa labaran Chinan sun ce mutum-mutumin da ke aikin ceton za su iya aika sakon hotunan bidiyo da hotuna kai tsaye, zuwa waje sannan suna da ababan kariya daga fashewar iskar gas.

    Bayan dakatar da aiki a mahakar an kuma umarci kamfanin da ke aiki a wajen Tongzhou Group, da ya dakatar da aikinsa a wasu wuraren uku da yake hakar ma'adanin kwal.

    An dai tsare shugaban kamfanin da wasu manyan jami'ai masu alaƙa da aikin.

  4. 'Kowane mataki za mu ɗauka sai da izinin jagoran addinin ƙasarmu'

    Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezhakian ya ce duk wani mataki da ƙasar za ta ɗauka dole sai da amincewar majalisar tsaron ƙasar da kuma jagoran addinin ƙasar.

    Yayin wata ganata wa daraktocin kafofin yaɗa labaran ƙasar, Mista Pezhakian ya ce a duk lokacin da aka cimma wata matsaya ta fuskar diplomasiyya, dole ne sai duka cibiyoyi da hukumomi da ƙungiyoyin ƙasar sun haɗu a kan murya ɗaya a kan kowane irin mataki.

    Ya kuma yi kira ga kafofin yaɗa labaran ƙasar su taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa haɗin kan jama'a da ƙarfafa matakan da gwamnati ke ɗauka da tallafa wa ci gaban ƙasar.

    Ganawar Shugaba Pezhakian da daraktocin yaɗa labaran ƙasar na zuwa ne kwana guda bayan wani ɗanmajalisar ƙasar ya yi iƙirarin cewa, shugaban ƙasar ya amince da yarjejeniyar dakatar da wuta ba tare da amincewa jagoran addinin ƙasar ba.

  5. 'Ebola ta kashe mutum fiye da 200 a larduna biyu na DR Kongo'

    Jami'an lafiya a Jamhuriyar Dimokradiyyar Kongo sun ce cutar Ebolar da ta ɓarka a yanzu ta haddasa mutuwar mutane fiye da 200 a larduna biyu.

    Haka kuma adadin waɗanda suka kamu da cutar ya ƙaru zuwa mutum fiye da 860.

    Akwai damuwar da ake da ita cewa jami'an lafiya da kuma ma'aikatarn agaji ba sa iya kai wa ga mutanen da cutar ta shafa bayan da 'yan tawayen M23, suka rufe babban filin jirgin saman da ke Goma, wato inda suke ajiye makamansu, lamarin da ya tursasawa ƙungiyoyi agaji komawa shiga ta yankin Kivu.

    Cutar Ebolar - da ta barke a Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo - ita ce mafi muni da ta barke a Afirka da ba a taɓa ganin irinta ba a tsawon shekara 10.

    A jiya Asabar ne, gwamnatin ƙasar ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a birnin Bunia da ke arewa maso gabashin ƙasar domin takaita haɗarin yaɗuwar cutar.

  6. An cimma matsayar kawo ƙashen yaƙin Iran - Trump

    Shugaba Trump na Amurka ya ce an cimma matsaya a kan yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin da ƙasarsa ke yi da Iran.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Mista Trump ya ce ya bayyana matakin ne bayan wayar da ya yi da shugabannin ƙasashen Larabawa a karo daban-daban da kuma Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu.

    Shugaban na Amurka ya ce cikin yarjejeniyar da aka cimma akwai batun sake buɗe mashigar Hormuz.

    Ya ce yanzu ana tattauna matakin ƙarshe na yarjejeniyar kuma nan ba da jimawa ba za a sanar da abin da aka cimma.

    To sai dai kafar yaɗa labaran Iran ta Fars, mai kusanci da dakarun juyin juya halin Iran, ta ce mashigar Hormuz za ta ci gaba da kasancewa a ƙarƙashin ikon Iran.

  7. Wani ɗan bindiga ya buɗe wuta a kusa da fadar gwamnatin Amurka

    Jami'an tsaro na sirri sun tabbatar da kisan wani ɗan bindiga da ake zargin ya buɗe wuta a kusa da fadar gwamnatin Amurka ta White House, bayan da suka yi musayar wuta da jamian tsaro na farin kaya.

    Jami'an sun ce mutumin da ake zargi sai da ya tunkari wani wajen binciken ababan hawa da ke kusa da ginin sannan ya buɗe wuta a kan jami'an tsaron da ke wajen.

    Ba tare da ɓata lokaci ba jami'an tsaron suka mayar masa da martani inda aka ji masa rauni shi da wani mutum da ke kusa da shi.

    An dai kai mutumin da ake zargi asibiti inda daga bisani kuma ya mutu. Lokacin da aka kai harin shugaba Trump na cikin fadar ta white house.

  8. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa barkanmu da hutun ƙarshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafa