Yau wa'adin Amurka ga Iran kan mashigar Hormuz zai ƙare
Yau ne ake sa ran wa’adin da Amurka ta bai wa Iran zuwa ƙarshen ranar yau Asabar zai ƙare, inda ta buƙaci Tehran ta ba da tabbacin cewa mashigar Hormuz za ta ci gaba da kasancewa a buɗe kuma ba za a kai hare-hare kan jiragen kasuwanci ba.
Jami’an Amurka sun ce Iran ta shaida musu a sirrance cewa wasu masu tsattsauran ra’ayi da ba sa aiki ƙarƙashin cikakken ikon gwamnati ne ke da hannu a hare-haren da aka kai kan wasu jiragen ruwa, da nufin kawo cikas ga tattaunawar da ake yi.
A daidai lokacin da ake fargabar ƙarin tashin hankali a yankin, Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya kai ziyara ƙasar Oman domin tattauna rikicin da ya shafi mashigar Hormuz.
Haka kuma, wata tawagar masu shiga tsakani daga Qatar ta gana da jami’an Iran a Tehran, a wani yunƙuri na hana rugujewar fahimtar juna tsakanin Iran da Amurka da kuma rage zafafan takun-saƙar da ke ƙara ƙamari a yankin.
Mashigar Hormuz na daga cikin manyan hanyoyin jigilar man fetur a duniya, kuma duk wani rikici a yankin na iya yin tasiri ga kasuwancin duniya da kuma farashin mai.