Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 10/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 10 ga watan Agustan 2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. Nijar ta gayyaci kamfanonin sufuri bayan hatsarin bas da ya kashe mutum 22

    Gwamnatin Nijar ta gayyaci kamfanonin sufuri biyu domin amsa tambayoyi bayan wani mummunan hatsarin bas da ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 22, ciki har da sojoji 17.

    Ma'aikatar Sufurin ƙasar ta ce motocin kamfanonin STM da SONITRAV ne suka yi karo da juna gab da ƙauyen Rezi a yankin Madaoua.

    Motar kamfanin SONITRAV na ɗauke da sojojin da ke dawowa daga horaswa.

    Baya ga mutum 22 da suka rasu, mutum 37 sun kuma jikkata.

    Hukumomi sun ce sun fara bincike kan musabbabin hatsarin tare da ɗaukar matakan hana irin haka a gaba.

    Hatsarin ya sake tayar da hankali kan matsalar haɗurran motoci a hanya a Nijar, inda ake yawan danganta su da gudun da ya wuce kima, take dokokin hanya da kuma lodin da ya wuce ƙa'id

  2. Iran ta naɗa Mohsen Rezaei wakilin Mojtaba Khamenei a majalisar tsaron ƙasar

    Sabon jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, a cikin wata wasiƙa da aka danganta da shi ya naɗa Mohsen Rezaei a matsayin wakilinsa a Majalisar Tsaron Ƙasar Iran.

    Sanarwar ta kuma yaba da gudunmawar Mohammad Baqer Zolghadr, wanda ake raɗe-raɗin zai sauka daga muƙaminsa na sakataren majalisar, tare da naɗa shi a matsayin mai ba da shawara kan harkokin siyasa.

    Baya ga Rezaei, Saeed Jalili ma wakilin Jagoran addini ne a majalisar, wadda Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ke jagoranta.

    A tsarin mulkin Iran, duk wani muhimmin ƙuduri na majalisar sai Jagoran ƙasar ya amince da shi kafin aiwatarwa.

    Mojtaba Khamenei, wanda ya gaji mahaifinsa bayan kashe shi, har yanzu bai bayyana a bainar jama'a ba, kuma saƙonnin da ake fitarwa da sunansa na rubuce ne kawai.

  3. Iran ta kwashe shekaru 51 tana nuna mugun hali - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Iran ta kwashe shekaru 51 tana nuna abin da ya kira “ɗabi’a mara kyau”.

    Trump ya bayyana hakan ne a shafinsa na Truth Social, inda ya wallafa jadawalin da ke nuna faduwar darajar kuɗin Iran, rial.

    A wani ɓangaren kuma, an naɗa Mohsen Rezaei a matsayin wakilin Jagoran Iran a Majalisar Tsaron Ƙasa ta Ƙoli, yayin da aka naɗa Shugaba Masoud Pezeshkian a matsayin sakataren majalisar.

    Haka kuma, babban hafsan sojojin Amurka ya ce tun bayan fara toshe harkokin ruwan Iran, sojojin ƙasar sun tilasta wa jiragen kasuwanci 55 sauya hanya, tare da tsayar da wasu jirage biyu ta hanyar harbe-harbe.

  4. 'Iran na ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa a mashigar Hormuz'

    Iran na ci gaba da kai hare-hare tare da tsaurara sa ido kan jiragen ruwa da ke bi ta mashigar Hormuz ba bisa ƙa'ida ba lamarin da ya sa Ƙungiyar Kula da Harkokin Teku ta Birtaniya (UKMTO) ta ce hare-haren na barazana ga zirga-zirgar jiragen daukon mai.

    A cikin sabon rahotonta na wata-wata, UKMTO ta bayyana cewa Iran ta kai hari kan wani tankar dakon mai na Hadaddiyar Daular Larabawa a ranar Asabar, abin da ya ƙara rage zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar zuwa kaɗan daga cikin jiragen da ke amfani da wannan muhimmiyar hanyar ruwa.

    Haka kuma, ƙungiyar ta ce ana ci gaba da ayyukan soja kai tsaye, ciki har da hare-haren makamai masu linzami da fashe-fashe a kusa da jiragen ruwa a hanyoyin ruwa da ke kudancin mashigar zuwa ƙasar Oman.

    UKMTO ta kuma yi gargaɗin cewa har yanzu akwai nakiyoyin ruwa da ba a gano ko kuma ba a tarwatsa ba a yankin, lamarin da ke ci gaba da barazana ga tsaron jiragen ruwa da harkokin kasuwanci a mashigar Hormuz.

  5. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.