Tinubu ya zaɓi ya yi hutu a daidai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasar - Atiku
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC a zaɓen 2027, Atiku Abubakar ya soki tafiyar da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya yi zuwa Turai na tsawon makwanni uku, yana mai cewa Tinubu ya zaɓi ya yi hutu a daidai lokacin da ƙasar ke cikin mawuyacin hali da ke buƙatar shugabanci.
Atiku ya ce duk da cewa shi ma ya taɓa yin tafiye-tafiye da zama a ƙasashen waje, akwai bambanci mai girma tsakanin tafiyar mutum mai zaman kansa da ta shugaban kasa mai ci.
A cikin sanarwar da ya fitar, Atiku ya ce ‘yan Najeriya na fama da tsadar rayuwa, inda farashin man fetur ya kai matakin da ya gagari talakawa, yayin da iyalai da dama ke fama da matsalar ciyar da kansu.
Ya kuma yi nuni da yadda kudin sufuri suka ƙaru, lamarin da ya sanya yin tafiya zuwa ƙauyuka da garuruwa ya zama ƙalubale ga mutane da dama.
Atiku ya ƙara da cewa "matsalar tsaro na ci gaba da jefa rayukan ‘yan Najeriya cikin hadari inda a irin wannan lokaci ne ya kamata shugaban kasa ya kasance tare da al’ummarsa."
Ya ce abin mamaki ne yadda Shugaba Tinubu ya bar ƙasar zuwa Turai a daidai lokacin da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, yake wata tafiya ta aiki a ƙetare.
Atiku ya ce shugabanci ba kawai mallakar ikon riƙe muƙami ba ne, har ila yau yana buƙatar sanin lokacin da kasa ke buƙatar shugabanta ya kasance a gida.
Atiku ya zargi gwamnatin Tinubu da gaza gano irin wahalhalun da ‘yan kasa ke ciki, yana mai cewa idan aka ba shi dama zai mayar da Najeriya kasa mai saukin rayuwa ga jama’arta.