Na cika kashi 90 cikin 100 Na alƙawuran da na wa mutanen Kano - Gwamna Abba
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta cika kusan kashi 90 cikin 100 na alƙawuran da ta yi wa al’ummar jihar cikin shekaru uku a kan mulki.
Ya yi wannan bayani ne yayin da ya karbi bakuncin Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru, wanda ya kai masa ziyarar Sallah a Fadar Gwamnatin Kano a ranar Asabar.
A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, ya ce gwamnatin Yusuf ta mayar da hankali kan aiwatar da ayyukan raya kasa da manufofi da suka shafi rayuwar al’umma kai tsaye a fannoni daban-daban.
Ya bayyana cewa an samu ci gaba a fannonin ilimi, lafiya, ababen more rayuwa, noma, samar da ruwa, tallafawa matasa da bunkasa tattalin arziki, tare da cewa duk wadannan na nufin inganta rayuwar jama’a da kuma ciyar da Kano gaba mai dorewa.
A nasa bangaren, Sarkin Rano ya yaba wa gwamnan bisa abin da ya kira manyan nasarori cikin shekaru uku, inda ya ambaci kammala hanyoyi mai tsawon kilomita biyar a Rano, Kibiya da Bunkure, da kuma ci gaban aikin ruwa na Kaluwaiwai.