Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Milner ya yi ritaya bayan shekara 24 yana taka leda

Wannan shafi ne da zai ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa daga Litinin 01 zuwa Lahadi 07 ga watan Yunin 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Iraq ta sanar da ƴan wasan da za su buga mata kofin duniya, Gasar kofin duniya

    Kocin Iraq, Graham Arnold, ya sanar ranar Litinin jerin ƴan wasa 26 da za su buga Kofin Duniya, inda ya dogara sosai da babban rukuni na ƴan wasan da suka taimaka wajen samun tikitin shiga gasar ta hanyar wasannin share fage a tsakanin nahiyoyi.

    Ɗan wasan da ke buga gaba, Aymen Hussein ana sa ran zai jagoranci gurbin kai hare-hare a tawagar Iraq a wasannin da za ta buga a Arewacin Amurka. Wannan tsohon ɗan wasan, wanda ake kallonsa a matsayin gwarzo, shi ne zai jagoranci sahun gaba tare da Ali Al-Hamadi na Ipswich Town da kuma matasan ƴan wasa masu basira da ya haɗa da Ali Jassim da kuma Youssef Amyn.

    Wani abin lura shi ne rashin sunan Dario Naamo daga cikin tawagar. An cire ɗan wasan Dundee, bayan da ya canza ƙasar da yake wakilta a wasannin ƙasa da ƙasa, bayan da ya taɓa bugawa Finland a matakin matasa.

    Zaɓin ƴan wasan tsakiya na Arnold ya ƙunshi ƙwararru da suka saba da ƙwallon ƙafa a Turai, inda Zidane Iqbal na Utrecht da Aimar Sher na Heerenveen ke kan gaba a jerin.

    Haka kuma, Arnold ya yanke shawarar barin mai tsaron raga, Kamil Saadi cikin tawagar atisaye a matsayin kariya idan aka samu rauni.

    Iraq na komawa gasar Kofin Duniya a karon farko cikin shekaru 40, bayan ta doke Bolivia da ci 2-1 a watan Afrilu domin samun tikitin ƙarshe.

    An saka su a Rukunin I tare da Faransa da Senegal da kuma Norway.

    Masu tsare raga: Fahad Talib, Jalal Hassan, Ahmed Basil

    Masu tsaren baya: Hussein Ali, Manaf Younis, Zaid Tahseen, Rebin Sulaka, Akam Hashem, Merchas Doski, Ahmed Yahya, Zaid Ismail, Frans Putros, Mustafa Saadoon

    Masu buga tsakiya: Amir Al Ammari, Kevin Yakob, Zidane Iqbal, Aimar Sher, Ibrahim Bayesh, Ahmed Qasim, Youssef Amyn, Marko Farji Masu cin ƙwallaye: Ali Jassim, Ali Al Hamadi, Ali Yousef, Aymen Hussein, Mohanad Ali

  2. , Daga Jaridu

    Kocin Arsenal, Mikel Arteta, ya nuna aniyar dauko dan wasan Aston Villa da Ingila Morgan Rogers, mai shekara 23, a kokarinsa na ci gaba da samun nasarar lashe gasar Premier, duk da cewa Paris St-Germain da ta lashe gasar zakarun Turai ita ma na zawarcinsa. (Mirror), external

    Manyan masu daukar ma'aikata a Real Madrid sun bukaci kungiyar ta nemi dan wasan Arsenal Declan Rice, sakamakon yadda dan wasan na Ingila mai shekaru 27 ya burge su kan jagoranci da kuma kwarewa.(Teamtalk), external

    Golan Liverpool Alisson, mai shekara 33, yana shirin fada wa sabon kocin kungiyar cewa yana son ya bar Anfield ya koma Juventus. (Gazzetta dello Sport - in Italian), external

    Manchester United na gab da kulla yarjejeniya da dan wasan Brazil Ederson, mai shekara 26, daga Atalanta kan kudi kusan fan miliyan 35. (Talksport), external

  3. Za a hana ƴan wasa zuwa wajen koci idan gola ya ji rauni a gasar kofin duniya, Gasar kofin duniya

    Za a hana ƴan wasa a gasar Kofin Duniya ta 2026 zuwa yankin masu horarwa, domin tattaunawa da koci a lokacin da mai tsaron raga ya ji rauni, kamar yadda shugaban alkalan FIFA, Pierluigi Collina, ya bayyana.

    Haka kuma, Hukumar Dokokin Kwallon Kafa ta Duniya (IFAB) ta amince da bukatar sauya tsarin VAR, domin a ba da damar duba kura-kuran da suka shafi ketar da aka yi wa ƴan wasa.

    Wannan tsarin da ake kira “goalkeeper tactical timeout” ya zama abin tattaunawa sosai a ƴan shekarun nan. Ana amfani da shi a wasu lokuta ne ta hanyar kociyoyi domin ba ƴan wasa sabbin umarni ko dabaru ko kuma rage karfin gwiwar abokan hamayya.

    A watan Nuwamba, kocin Leeds United, Daniel Farke, ya zargi mai tsaron ragar Manchester City, Gianluigi Donnarumma, da yin kamar ya ji rauni domin “karkatar da dokoki” da kuma dakatar da wasa na ɗan lokaci.

    A irin wannan yanayi, mai tsaron raga kan zauna a kasa ya nuna alamar neman a duba lafiyarsa, sauran ƴan wasa su tafi wajen koci domin samun sabon umarni, sannan da zarar an gama bayanin, mai tsaron ragar zai tashi ya ci gaba da wasa kamar yadda aka saba.

  4. Har yanzu Wiliiams na jin raɗaɗin da kasarsa ba za ta buga gasar kofin duniya ba, Gasar kofin duniya

    Neco Williams ya amince cewa rashin zuwa buga gasar cin Kofin Duniya ta bana har yanzu yana ci masa rai, domin ya yi imanin Wales za ta iya yin tasiri a gasar da za a yi a Amurka da Canada da kuma Mexico.

    Wales ta rasa damar zuwa gasar karo na biyu a jere bayan ta sha kashi a wasan neman cike gurbi a hannun Bosnia-Herzegovina.

    Wannan rashin nasara ta fi taɓa zuciyar ɗan wasan baya na Nottingham Forest, Neco Williams, musamman ganin cewa shi ne ya kasa cin fenariti mai muhimmanci a karawar.

    Sai dai duk da wannan ci gaba da takaici, ɗan wasan mai shekara 25 ɗin ya ce wasannin sada zumunta da Ghana da Romania a wannan mako su ne matakin farko na ci gaba da huce wannan raɗaɗi, yayin da tawagar ke mai da hankali kan gasar Euro 2028 da za a yi a gida.

    Wasan da za su buga da Ghana a Cardiff ranar Talata zai zama abin tunawa da abin da suka rasa, domin Ghana na shirin shiga rukunin gasar World Cup ɗin da Ingila za ta kasance a ciki.

  5. , Daga Jaridu

    Dan wasan Portugal Joao Palhinha, mai shekara 30, ba ya son aron da aka ba da shi daga Bayern Munich zuwa Tottenham ya koma na dindindin kuma zai yi kokarin ganin ya koma Sporting a maimakon haka. (A Bola - in Portuguese), external

    Manchester United da Chelsea da Arsenal da Tottenham da Liverpool da kuma Newcastle dukkaninsu na zawarcin dan wasan AC Milan da Portugal Rafael Leao inda dan wasan mai shekara 26 na son ya bar San Siro a wannan bazara . (Calciomercato - in Italian), external

    Paris St-Germain ta fasa daukar dan wasan Atletico Madrid Julian Alvarez, sai dai dan wasan Argentina mai shekara 26 na jan hankalin Arsenal da Barcelona. (Mundo Deportivo - in Spanish), external

    An yi wa Inter Milan tayin dan wasan Manchester United Harry Maguire sai dai kungiyar ta Italiya ba ta dauki daukar dan wasan Ingila mai shekara 33 a matsayin wani abu da za ta ba fifiko ba (Gazzetta dello Sport via Football Italia), external

  6. Watakila Palace ta ɗauki Sage a matakin sabon koci, Premier League

    Ana sa ran kocin Lens, Pierre Sage, zai tattaunawa da Crystal Palace a farkon wannan mako yayin da ƙungiyar Premier League ke neman wanda zai maye gurbin Oliver Glasner.

    Palace (wanda ake yi wa lakabi da Eagles) na fuskantar kalubale a kokarin ɗaukar Andoni Iraola, wanda ake sa ran zai fara tattaunawa a hukuma da Liverpool a kwanaki masu zuwa domin maye gurbin Arne Slot da aka kore a ranar Asabar.

    Palace wadda ta lashe Conference League ta gabatar da tayin aiki mai tsoka ga Iraola, amma da alama yana kan hanyar zuwa wani wuri, yanzu Crystal Palace na duba wasu zaɓuɓɓuka daban.

    Ƙungiyar ta kudancin London, ƙarƙashin jagorancin shugaba, Steve Parish, ba zai yi gaggawa wajen yanke hukunci ba kan sabon koci, domin suna nazarin wasu sunaye daban.

    Daga cikin waɗanda ake dubawa akwai Sage, wanda ya yi suna a matsayin ɗaya daga cikin masu horarwa masu hazaka a Turai.

    BBC Sport ce ta fara bayyana sha’awar Crystal Palace ga mai shekara 47 a ranar 8 ga Mayu, amma a lokacin shugabancin Palace ya fi mayar da hankali kan ƙoƙarin ɗauko Iraola daga Bournemouth.

    Rahotanni sun ce kocin Lens ɗin da yiwuwar komawa Palace, kuma ana sa ran zai gana da jami’an ƙungiyar a cikin kwanaki masu zuwa.

  7. , Daga Jaridu

    Dan wasan Portugal Bernardo Silva, mai shekara 31, yana sha'awar komawa Barcelona ya yin da kwantiraginsa a Manchester City na gab da karewa.(Mundo Deportivo - in Spanish), external

    Brighton za ta fuskanci hamayya daga Hoffenheim da Eintracht Frankfurt wajan sayen dan wasan Wolfsburg Patrick Wimmer mai shekaru 25 .(Florian Plettenberg), external

    Crystal Palace ta sake tattaunawa da kocin Lens Pierre Sage da ake ganin yana da kwarewa sosai .(Mail), external

    Kocin Como Cesc Fabregas na jin dadin aikinsa a kungiyar Italiya duk da cewa an alakanta da shi da wasu ayuikam horas dayan wasa a wasu wurare ciki harda Real Madrid (Sport - in Spanish)

  8. Slot ya ce ya bar Liverpool a gurbin da ta dace, Liverpool

    Arne Slot ya ce ya bar Liverpool “daidai inda ya kamata ta kasance: cikin manyan ƙungiyoyin Turai” bayan da aka kore shi daga aikin koci ranar Asabar.

    Ɗan kasar Netherlands mai shekara 47 ya lashe kofin Premier League a kakar sa ta farko, amma shugabancin ƙungiyar ya yanke shawarar korarsa, bayan da Liverpool ta kare a matsayi na biyar a gasar bana, inda ta kasance da tazarar maki 25 tsakaninta da Arsenal wadda ta lashe kofin a karon farko bayan shekara 22.

    Liverpool za ta fara tattaunawa a hukumance a wannan mako da tsohon kocin Bournemouth, Andoni Iraola, kan yiwuwar ya maye gurbin Slot a matsayin sabon koci.

    A cikin wata buɗaɗɗiyar wasika mai cike da tausayi da aka buga a Liverpool Echo, Slot ya ce magoya baya sun tarbe shi cikin murna tun farko kuma sun taimaka masa wajen gudanar da aikinsa. Ya ce “Wannan abu ne da ba zan manta da shi ba,” in ji shi.

    Ya kara da cewa: “Na bar ƙungiyar da cikakken tabbaci game da abin da ke gaba.”

    “’Ƴan wasan da yawa sun yi hidima sosai, sun kiyaye darajojinsa kuma suka samar da lokuta masu ban mamaki, sun gina tushe mai ƙarfi da zai dawwama.”

    Duk da cewa Liverpool ta sha kashi sau 20 a dukkan fafatawa a bana, Slot ya tabbatar da cewa Liverpool ta samu gurbin shiga Champions League na kakar gaba.

    “Samun gurbin Champions League wani muhimmin nauyi ne kuma ya tabbatar Liverpool za ta ci gaba da fafatawa a matakin koli a kakar gaba da ma bayan haka,” in ji shi.

    “Lokacin da na fara tsayawa a matakin kociyan Liverpool, na san abin da wannan ƙungiyar ke bukata. Na kuma san cewa ba mu daina kokari ba.”

    Slot ya maye gurbin Jürgen Klopp a Liverpool a shekarar 2024 bayan kocin Jamus ɗin ya sauka daga mukaminsa bayan shekaru tara.

    Ya fara aikinsa cikin nasara sosai, inda ya jagoranci Liverpool zuwa kofin Premier League na 20, har ma da tazarar maki huɗu kafin ƙarshen kakar wasa a gaban magoya baya a Anfield.

  9. Milner ya yi ritaya bayan shekara 24 yana taka leda, Premier League

    Tsohon ɗan wasan tawagar Ingila, James Milner, ya sanar da yin ritaya daga buga ƙwallon ƙafa bayan ya shafe shekara 24 yana taka leda a gasar Premier League.

    Milner mai shekara 40, wanda ke iya taka leda a wurare daban-daban a fili, ya zauna ba tare da kwantiragi ba bayan shekara uku da suka gabata a Brighton & Hove Albion.

    A tsawon rayuwarsa ta ƙwallon ƙafa, Milner ya buga ƙungiyoyi shida wasa a gasar Premier League, kuma a watan Fabrairu ya kafa tarihin ɗan wasan da ya fi kowa yawan buga wasanni a gasar.

    Ya fara sana’arsa ne ta taka leda a Leeds United, sannan ya lashe kofin Premier League sau uku – guda biyu tare da Manchester City da kuma sau ɗaya tare da Liverpool. Haka kuma ya taimaka wa Liverpool ta ɗauki gasar UEFA Champions League a shekarar 2019.

    Milner ya fara buga wa Ingila wasa a shekarar 2009 lokacin yana tare da Aston Villa, ya yi wa tawagar kasar wasa 61.

    Milner ya fara bugawa Leeds United wasa yana ɗan shekara 16 a watan Nuwamban 2002. A lokacin, shi ne ɗan wasa na biyu mafi ƙarancin shekaru da ya taba buga Premier League.

    A wata mai zuwa kuma, ya zama mafi ƙarancin shekaru da ya ci ƙwallo a tarihin Premier League. A yanzu yana matsayi na uku bayan Max Dowman da James Vaughan.

    Rauni ya sa Milner ya rasa mafi yawan wasannin a kakar 2024-25, amma ya dawo ya buga karawa 22 a dukkan fafatawa a kakar 2025-26. Wasansa na ƙarshe a Premier League ya kasance na 658, wanda ya buga a ranar ƙarshe a kakar wasa da Brighton.

    Bayan shekara biyu a babbar ƙungiyar Leeds, an sayar da shi zuwa Newcastle United bayan Leeds ta faɗa gasar Championship a shekarar 2004.

    Daga nan ya koma Aston Villa a 2008, sannan Manchester City a 2010, inda ya taimaka musu wajen lashe kofunan Premier League na farko a shekarun 2012 da 2014.

    A shekarar 2015 ya koma Liverpool, inda ya shafe shekaru takwas a filin Anfield, ya zura ƙwallaye 26 a wasa 332.

    A shekarar 2020, ya taimaka wa Liverpool lashe kofin Premier League na farko tun 1990. Haka kuma ya lashe kofin FA Cup da League Cup tare da Liverpool da Manchester City.

  10. Barkanmu da shiga fagen labarin wasanni

    Jama'a barkanmu da kasancewa a cikin shirin labarin wasanni da za mu ke sanar da ku wainar da ake toyawa daga wannan ranar zuwa Asabar 18 ga watan Afirilu.

    Sunana Mohammed Abdu za ku iya tafka muhawara a BBC Hausa Facebook ko kuma ku bibiyi labaran da muke wallafawa a BBC Hausa WhatsApp.