Shugaba Ramaphosa na fuskantar kiraye-kirayen ya yi murabus
Kotun Kundin Tsarin Mulki a Afirka ta Kudu ta umarci majalisar dokoki da ta kafa kwamiti da zai yi bincike kan Shugaba Cyril Ramaphosa kan sama da faɗi da fiye da dala 500,000 daga gidansa da ke ƙauye shekaru shida da suka gabata.
Lamarin ya janyo zarge-zarge cewa shugaban ya gaza bayyana ta inda kuɗin ya fito.
Kotun ta yanke cewa majalisar ta ɗauki matakin da ya saɓa doka ta hanyar toshe yunƙurin tsige shugaban a 2022. A lokacin ƴanmajalisa sun kaɗa ƙuri'ar ƙin amincewa da wani rahoton kwamiti mai zaman kansa da ya gano cewa akwai dalilan da za su saka Mista Ramaphosa ya amsa tambayoyi game da satar.
A lokacin jam'iyyar Mista Ramaphosa ta ANC ce take da rinjaye, matsayin da ta rasa a zaɓen da ya gabata.
Matakin Kotun Tsarin Mulkin ta sa jagoran adawa a ƙasar, Julius Malema kira ga Shugaba Ramaphosa da ya sauka daga kan mulki.
Malema ya yi maraba da hukuncin kotun yana mai cewa ya kamata Ramaphosa ya yi murabus sannan ya mayar da hankali kan shirye-shiryen tsige shi saboda hakan na da mummunan tasiri a kansa.