Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Juma'a 08/05/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Aisha Aliyu Jaafar da Nabeela Mukhtar Uba

  1. Shugaba Ramaphosa na fuskantar kiraye-kirayen ya yi murabus

    Kotun Kundin Tsarin Mulki a Afirka ta Kudu ta umarci majalisar dokoki da ta kafa kwamiti da zai yi bincike kan Shugaba Cyril Ramaphosa kan sama da faɗi da fiye da dala 500,000 daga gidansa da ke ƙauye shekaru shida da suka gabata.

    Lamarin ya janyo zarge-zarge cewa shugaban ya gaza bayyana ta inda kuɗin ya fito.

    Kotun ta yanke cewa majalisar ta ɗauki matakin da ya saɓa doka ta hanyar toshe yunƙurin tsige shugaban a 2022. A lokacin ƴanmajalisa sun kaɗa ƙuri'ar ƙin amincewa da wani rahoton kwamiti mai zaman kansa da ya gano cewa akwai dalilan da za su saka Mista Ramaphosa ya amsa tambayoyi game da satar.

    A lokacin jam'iyyar Mista Ramaphosa ta ANC ce take da rinjaye, matsayin da ta rasa a zaɓen da ya gabata.

    Matakin Kotun Tsarin Mulkin ta sa jagoran adawa a ƙasar, Julius Malema kira ga Shugaba Ramaphosa da ya sauka daga kan mulki.

    Malema ya yi maraba da hukuncin kotun yana mai cewa ya kamata Ramaphosa ya yi murabus sannan ya mayar da hankali kan shirye-shiryen tsige shi saboda hakan na da mummunan tasiri a kansa.

  2. Jihohi 18 na cikin haɗarin fuskantar ambaliya a Najeriya - Nimet

    Hukumar kula da yanayi ta Najeriya Nimet ta yi gargaɗi cewa akwai yiwuwar jihohi 18 a ƙasar su fuskanci ambaliya cikin kwanaki masu zuwa sakamakon ruwa kamar da bakin ƙwarya da ake tsammanin yi.

    A wata sanarwar gargaɗi da ta wallafa a shafinta na X jiya Alhamis, Nimet ta ce jihohin da ka iya fuskantar ambaliyar sun haɗa da Zamfara da Nassarawa da Kwara da Oyo da Legas da Ogun da Ekiti da Delta da Imo da Anambra da Enugu da Ebonyi da Akwa Ibom da Cross River da Rivers da Edo da Ondo da Bayelsa.

    A cewar hukumar, ambaliyar na iya janyo tsaiko wajen wucewar motoci da yin ɓarna ga wasu gidaje da gonaki da gine-gine sai toshewar magudanan ruwa da rashin lantarki da matsalar sadarwa da kuma haɗurran yaɗuwar cututtuka.

    Nimet ta kuma shawarci jama'a da ke jihohin da su ɗauki matakan da suka dace ta hanyar tsaftace magudanan ruwan da ke gidajensu sannan kuma su riƙa duba hasashen yanayi a kai a kai.

    Hukumar ta gargaɗi masu ababen hawa da masu tafiya a ƙafa da su kaucewa yin tuƙi ko ma bi ta wuraren da ambaliya ta mamaye.

    Gargaɗin na zuwa ne bayan da gwamnatin ƙasar ta yi gargaɗi cewa wasu jihohi 33 har da birnin tarayya Abuja na cikin haɗarin fuskantar ambaliya a 2026.

  3. Mayaƙan ISWAP sun kashe sojojin Najeriya biyu a Borno

    Mayaƙan ISWAP sun halaka sojojin Najeriya biyu da ke aiki ƙarƙashin rundunar Haɗin Kai a Magumeri da ke jihar Borno.

    Lamarin ya faru ne yayin da dakarun da ke aiki ƙarƙashin rundunar suka daƙile wani harin ISWAP, abin da ya yi sanadin mutuwar ƴan ta'adda da dama har ma ta kai ga ƙwato makamai daga hannunsu.

    Bayanin hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Leftanar Kanar Sani Uba ya fitar wanda shi ne jami'in yaɗa labarai na rundunar Operation Haɗin Kai.

    Samamen dai ya faru ne da sanyin safiyar Alhamis lokacin da ƴan ta'adda suka yi yunƙurin mamaye wani sansani na rundunar.

    Rundunar soji ta ce sojoji sun kai martani cikin sauri lamarin da ya sa suka daƙile harin tare da kashe mayaƙan da dama.

    Daga cikin makaman da sojojin suka ƙwato a hannun mayaƙan akwai bindigoyi ƙirar PKT da AK47 da kuma tarin alburusai.

    A cewar sanarwa, soja guda da wasu da suka ji rauni na samun kulawa.

  4. Ana tuhumar wasu mata ƴan Australiya masu alaƙa da IS da laifin mallakar baiwa

    Wasu mata biyu da aka alaƙanta da ƙungiyar IS - mai iƙirarin jihadi - waɗanda suka koma ƙasar Australiya daga Syria sun bayyana a kotu a kan tuhumarsu da aikata laifuka da suka haɗa da mallakar baiwa.

    Ana zargin Kawsar Abbas mai shekara 53 da sayen wata mata 'yar Yazidi a matsayin baiwa, tare da ajiye ta a gidanta.

    Ita ma 'yar Kawsar dɗin, Zeinab Ahmed - ana tuhumarta da irin waɗannan laifuka biyu.

    Akwai wasu matan biyu su ma da suka koma Australiya ranar Alhamis - ɗaya ba a tuhume ta ba tukunna, yayin da aka tuhumi ɗayar da kasancewa 'yar ƙungiyar ta'addanci.

  5. Chadi ta ayyana dokar ta ɓaci kan kisan sojinta 26

    Chadi ta ayyana kwana 21 na dokar ta ɓaci a yankin Tafkinta bayan harin da ƙungiyar Boko Haram ta kai a farkon makon nan, inda ta kashe aƙalla sojoji 26.

    Tuni ƙasar ta yankin Tsakiyar Afirka ta ayyana zaman makoki, bayan da mayaƙan Boko haram suka kashe wasu janar-janar na sojinta biyu a ranar Laraba, a lokacin da suke sintiri a wasu tsibirai a yankin tafkin.

    Kafin wannan, ƙungiyar ta kashe sojoji 24 a wani hari da ta kai wani sansanin sojin ƙasar.

  6. An yi musayar wuta tsakanin Amurka da Iran a Mashigar Hormuz

    Shugaba Donald Trump ya ce har yanzu yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta na nan daram - duk da ɗauki ba daɗi da aka yi tsakanin jiragen yaƙin ruwa na Iran da Amurka a Mashigar Hormuz.

    Wakilin BBC ya ce Amurka da Iran na zargin juna da fara buɗe wuta

    Sojojin Amurka sun ce Iran ce ta harba makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa da wasu ƙananan jiragen ruwa a kan jiragen ruwanta na yaƙi uku kan abin da Amurkar ta kira haka siddan ba takala.

    Ta ce a kan haka ne ta mayar da martani da hari kan kayan sojin Iran ɗin.

    Iran ta ce ta mayar da martani ne a kan barazanar sojin Amurka a kan jirgin ruwanta na dakon mai da kuma wani jirgin dakon.

    A halin da ake ciki kuma Haɗaɗɗiyar daular larabawa ta ce ta tare wasu makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa da Iran ta harba mata.

  7. Barka da Juma'a

    Masu bibiyar shafin BBC Hausa kai-tsaye, muna muku barka da zuwa shafinmu na yau Juma'a.

    Kamar kullum, za mu kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a duniya, kama daga yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran, da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta - Facebook da Instagram da YouTube da kuma X domin kallon bidiyo da kuma tafka muhawara.