Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 25/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 25 ga watan Agusta, 2026.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi

  1. Dakarun Amurka sun fara horas da na Najeriya a Bauchi

    Dakarun Amurka sun fara horas da twakwarorinsu na Najeriya kan yadda ake sarrafa jirage marasa matuƙa da kuma kula da sojojin da suka samu rauni a lokacin yaƙi a wani ɓangare na alaƙar tsaro da ƙasashen biyu suka ƙulla.

    A wani bayani da rundunar tsaron Amurka da ke da mazauni a Afirka ta wallafa a shafinta, Africom ta ce horon wanda ke gudana a jihar Bauchi da ke arewa maso gabashin Najeriya na mayar da hankali ne wajen tabbatar da cewa dakarun Najeriya sun laƙanci kasancewa cikin yanayin ko-ta-kwana da kuma bunƙasa yadda suke aiki.

    Rahoton na Africom ya ce horon ya mayar da hankali kan sarrafa jirage marasa matuƙa, sarrafa makamai, cire bama-bamai, kula da waɗanda suka ji rauni da kuma dabarun yaƙi ga ƙaramar tawagar soji.

    "Amurka da Najeriya na gudanar da aikin bayar da horo a sansanin horon soji da ke a Bauchi, Najeriya, bisa manufar musayar ƙwarewa, ƙarfafa abokan hulɗa da kuma yauƙaƙa alaƙa tsakanin ɓangarorin biyu," a cewar bayanin.

    Horon na zuwa ne bayan a watan Yuli Amurka ta sanar da janye akasarin dakarunta da ta tura Najeriya domin wani aikin yaƙi da ta'addanci na musamman, yayin da ƙasashen biyu suka ci gaba da shirinsu na musayar bayanan sirri da tsaro.

    A ƙarshen shekarar 2025 ne ƙasashen biyu suka ƙulla wata alaƙa ta tsaro bayan shugaban Amurka Donald Trump ya yi zargin cewa ana gallaza wa Kiristoci a Najeriya tare da matsa wa hukumomin Najeriyar lamba kan su magance matsalar tsaro.

  2. An samu nasara a tattaunawar sulhu da Iran - Pakistan

    Pakistan ta ce an samu gagarumar nasara a tattaunawar da wakilanta suka yi da shugabannin Iran a Tehran, wadda ta mayar da hankali kan hanyoyin samar da zaman lafiya.

    Shugaban hafsoshin sojin Pakistan, Field Marshal Asim Munir, ne ya jagoranci tawagar kasar a ziyarar.

    Rahotanni sun ce tattaunawar da ya yi da shugaban Iran da ministan harkokin wajen kasar da kuma shugaban majalisar dokoki ta mayar da hankali ne kan matakan dakile ci gaba da rikicin, da sake bude Mashigar Hormuz, da kuma neman hanyoyin kawo karshen yaƙin da ake yi tsakanin Iran din da Amurka.

    An kuma ruwaito cewa Field Marshal Munir ya tuntuɓi Shugaban Amurka, Donald Trump, kafin tafiyarsa Tehran.

    Rahotanni sun ce Amurka ta nemi Pakistan ta yi amfani da tasirinta wajen shawo kan Iran ta koma teburin tattaunawa.

    Sai dai kawo yanzu babu wata sanarwa daga Washington game da sakamakon ganawar.

  3. 'Takunkumi ba sabon abu ba ne a wurinmu'

    Iran ta mayar wa da Amurka martani da cewa, Amurkar ta daɗe ba ta tsaurara mata takunkumin tattalin arziƙin da take mata barazana da shi ba, tana mai cewa tana da ƙwarin gwiwa cewa abokan hulɗar kasuwancinta za su bijire wa duk wani matsin lamba daga Washington.

    Ministan kudin Iran, Ali Madanizadeh, ya ce takunkumi ba sabon abu ba ne ga ƙasarsa.

    Ya ce, idan maƙiyan ƙasar suka ƙaddamar da abin da ya kira "ta'addancin tattalin arziƙi", Iran ma tana da nata hanyoyin mayar da martani kuma ta san yadda ake takun-saƙar - ba layance mata za a yi ba.

    Shugaban majalisar ƙoli ta tsaron Iran, Mohsen Rezaei, ya yi gargaɗin cewa Tehran a shirye take ta dakatar da dukkan fitar da man fetur daga ƙasashen yankin Tekun Fasha.

    A jiya Litinin Sakataren Baitulmalin Amurka, Scott Bessent, ya ce bankuna da kamfanoni da kuma ƙasashen da suka ci gaba da hulɗa da Iran za su fuskanci irin yadda ake mayar da Iran saniyar-ware a fannin tattalin arziƙi, idan suka ki katse dangantakarsu da ita.

  4. Barka da Maulidi!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata a wannan shafi na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook, instagram da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.