Mutum 60 sun rasu a arangamar yau a Yemen
Arangamar da aka yi tsakanin dakarun gwamnatin Yemen da Saudiyya ke goyon baya da kuma mayaƙan Houthi ta yi sanadiyar mutuwar sama da mutum 60, kamar yadda majiyoyin lafiya da na soji suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP.
Rahoton ya ce fararen hula ma na cikin waɗanda suka mutu.
AFP ta ruwaito cewa dakarun gwamnati 26 sun mutu a cikin sa'o'i da dama na faɗa a yankin kudu maso yammacin Yemen.
Majiyoyin lafiya da na soji na ƙungiyar Houthi, wadda Iran ke goyon baya, sun kuma ce an kashe mayaƙansu 31 a arangamar.
Wata majiya daga ɓangaren lafiya a birnin Taiz, wanda ke ƙarƙashin ikon gwamnati, ta ce wani hari da makami mai linzami ya kai wa wata motar bas ya kashe fararen hula shida tare da raunata wasu bakwai.
Ƙungiyar Houthi, wadda ke kiran kanta Ansar Allah, tana iko da wani babban yanki na arewaci da gaɓar tekun Yemen da ke kan Tekun Bahar Maliya, tare da babban birnin ƙasar, Sanaa.
Kwamitin Shugabancin Yemen, wanda ƙasashen duniya suka amince da shi a matsayin gwamnatin ƙasar, na samun goyon bayan Saudiyya. Yana iko da gabashin Yemen da kuma gaɓar tekun kudancin kasar, ciki har da tashar jiragen ruwa ta Aden.