Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, 09/05/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, 09/05/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Mutanen da suka kamu da cutar Hantavirus a duniya sun kai 8; uku sun mutu - WHO

    Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar da cewa mutum takwas sun kamu da cutar Hantavirus a duniya, inda uku suka mutu.

    Kamar yadda sabbin bayan da WHO ta fitar a ranar Juma'a suka nuna, ta ce akwai barazanar ɓarkewar annobar a faɗin duniya amma za ta ci gaba da nazarin lamarin.

    Hantavirus ƙwayoyin cuta ne na zoonotic waɗanda ke iya yaɗuwa zuwa mutane.

    WHO ta ce an tabbatar da mutum shida da suka kamu da kwayar cutar Andes, inda mutum hudu suke kwance a asibiti, sai kuma mutum guda da ya warke.

    "Waɗanda suka kamu da cutar na fama da zazzabi, sanyi a gaɓoɓin jiki, rashin natsuwa da figici, matsanancin damuwa na shan wahala wajen numfashi," in ji WHO.

  2. Jam'iyar Labour ta faɗi zaɓe a Lewisham a karon farko cikin shekaru 55

    Jam'iyyar Green Party ta Birtaniya ta lashe zaɓen ƙaramar hukumar Lewisham inda ta kayar da Labour da ta shafe tsawon shekaru tana mulki.

    A yanzu dai jam'iyyar Greens ta lashe aƙalla kujeru 28 daga cikin 54, inda hakan ya ba su gagarumin rinjaye, kuma har yanzu ana jiran sakamakon gundumomi 19.

    Labour ta lashe kujeru tara zuwa yanzu.

    Babu wata jam’iyya da ta taɓa lashe zaɓen yankin bayan Labour a tsawon shekaru 55, tun bayan gwamnatin Conservative ta shekarar 1971.

  3. "Saboda haɗin kan ƙasa ne na amince a mayar da takarar shugaban ƙasa kudu"

    Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Kwankwaso, ya ce ya goyi bayan matakin da jam’iyyar NDC ta yanke na keɓe tikitin takarar shugaban Najeriya a 2027 zuwa yankin Kudancin ƙasar,

    Kwankwaso ya ce matakin ya nuna yadda jam’iyyar ke raba madafun iko da kuma tabbatar da adalci.

    Kwankwaso ya bayyana haka ne a wajen babban taron jam’iyyar na ƙasa da aka gudanar a Abuja, inda ya yi jawabi ga wakilai da magoya bayansa da kuma masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

    Ya ce, “Ina goyon bayan matakin keɓe tikitin takarar shugaban ƙasa zuwa Kudu domin yankin ya kammala shekarunsa takwas.

    "Wannan ita ce matsayar jam'iyyar kan tsarin karɓa-karɓa."

    Ya kuma buƙaci ‘yan Najeriya da magoya bayan NDC su wayar da kan al'umma game da manufofin jam’iyyar a yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.

    Kalaman nasa na zuwa ne jim kaɗan bayan da NDC ta amince da miƙa tikitin takarar shugaban ƙasar a shekarar 2027 a Kudancin Najeriya na tsawon shekaru huɗu kawai.

  4. Kwankwaso ya yi magana kan binciken ɓatan Dadiyata

    Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ya yi farin ciki da umarnin da Babban Sufeton Ƴansandan Najeriya, Olatunji Disu ya bayar na gudanar da bincike kan ɓacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.

    A ranar Juma’a ne IGP Disu ya ba da umarnin a yi bincike kan zargin da wani mai suna Muhammad Musa Kamarawa, ya yi na cewa wasu jami’ai biyu, CSP Hussaini Gimba da CSP Hassan Gimba, suka kashe Dadiyata da wani mutum mai suna Saminu S/Fada Gusau, a Kaduna.

    Musa ya yi iƙirarin cewa "a gaban idonsa aka kashe Dadiyata". Tuni batun ya ɗauki hankali a shafukan sada zumunta.

    A wani sako da Kwankwaso ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce yana kwarin gwiwa kan matakin da IGP ya ɗauka na binciken zargin da ake yi cewa ƴansandan biyu na da alaƙa da sace ɗan gwagwarmayar.

    “Tun da aka sace shi a shekarar 2019, ni da ƴan'uwa muke ta addu’a tare da kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike tare da gurfanar da waɗanda ke da hannu a bacewarsa a gaban kotu,” in ji Kwankwaso.

    Ya bukaci ƴansanda su sa ido kan jami’an da ake zargi don hana yin katsalandan a binciken, inda ya yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da cewa an biya iyalan Dadiyata diyya kan halin da aka jefa su.

    Dadiyata fitaccen mai sharhi a shafukan sada zumunta da ya yi ƙaurin suna wajen sukar manufofin gwamnatin Kano ta wancan lokacin ƙarƙashin gwamna Abdullahi Ganduje.

    A watan Agustan 2019 ne wasu da ba a san ko su waye ba suka sace shi daga gidansa da ke Barnawa, Kaduna, kuma har yanzu ba a san inda yake ba bayan shekaru bakwai.

  5. Hotunan yadda jam'iyyar NDC ke gudanar da babban taronta na ƙasa a Abuja

    Jam'iyyar NDC mai hamayya a Najeriya na gudanr da babban taronta na ƙasa a Abuja, babban birnin ƙasar.

    Ɗaruruwan mayoya bayan jam'iyyar ne suka taru a aharabar filin taron da ke tsakiyar birnin Abuja.

    Hon. Nasiru Yusuf Gawuna, wanda tsohon ɗan takarar gwamnan Kano a zaɓen 2023 ne na daga cikin ƴayan jam'iyyar ta NDC.

    Taron jam'iyyar na ziuwa ne mako guda bayan da Peter Obi da Kwankwaso suka koma cikinta bayan ficewarsu daga NDC

  6. Najeriya ta ƙarfafa ƙawancen tsaronta da Amurka

    Najeriya da Amuka sun amince da ƙarfafa haɗin kan tsaro tsakaninsu domin yaƙi da ta'addanci.

    Cikin wata sanarwa da kakain shugaban ƙasar Bayo Onanuga ya fitar, ya ce an cimma hakan ne a ganawar da mai taimaka wa shugaban ƙasar kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu ya yi da mataimakin shugaban Amurka, JD Vance da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio a birnin Washington.

    Ganawar na zuwa ne yayin da ake fargabar ƙaruwar ƙaruwar matsalar tsaro a wasu sassan arewa ta tsakiyar ƙasar, lamarin da ya haifar da ƙarin matsin lamba daga gwamnatin Amurka.

    A ranar Juma'a sojojin ƙasar suka ce sun kashe mayaƙan ISWAP aƙalla 50 a wani hari da suka yi niyyar kai wa sansaninsu a jihar Yobe.

    Gwamnatin Najeriya dai ya musanta cewa ana ƙaddamar da hare-haren ne domin muzguna wa wani addini na daban.

  7. Bahrain ta kama wasu da take zargi da kasancewa mambobin IRGC na Iran

    Ma'aikatar cikin gida ta Bahrain ta ce ta kama mutum 41 da take zargi da alaƙa da rundunar juyin juya halin Iran.

    An kuma zargi mutanen ta nuna goyon baya ga abin da hukumomin Bahrain suka kira hare-haren Iran

    Iran ta riƙa harba makamai masu yawa zuwa cikin Bahrain da sauran ƙasashen yankin Gulf, bayan da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar da hare-hare kan Iran a ƙarshen watan Fabrairun.

    Duka ɓangarorin biyu a yanzu na aiki da yarjejeniyar dakatar da wuta, wadda Pakistan ke ƙoƙarin shiga tsakani.

  8. Jam'iyyar NDC na gudanar da babban taronta na ƙasa

    Jam'iyyar hamayyar ta NDC a Najeriya na gudanar da babban taronta na ƙasa domin zaɓen sabbin shugabanninta.

    Matakin na zuwa ne mako guda bayan da manyan jiga-jigan siyasar ƙasar biyu, Peter Obi da Kwankwaso suka sanar da komawa cikinta.

    Ɗaruruwan magoya bayan jam'iyyar ne suka taru a harabar wurin gudanar da taron a Abuja.

    Akwai bayanai masu ƙarfi da ake yaɗawa cewa Peter Obi da Kwankwaso ne jam'iyyar za ta bai wa takarar shugaban ƙasar a jam'iyyar.

  9. EFCC ta ayyana neman Sadiya Farouq ruwa a jallo

    Hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta ayyana neman tsohowar ministar jin ƙai ta ƙasar, Sadiya Umar Farouq ruwa a jallo.

    Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na internet, ta ce tana neman tsohuwar ministar bisa zarge-zargen laifukan haɗa baki domin aikata laifuka da amfani da ofishi ba bisa ƙa'ida ba da karkatar da kuɗin gwamnati.

    Sanarwar EFCCn ta buƙaci jama'a su sanar da hukumar duk inda suka ga tsohuwar ministan domin kama ta.

    Sadiya Umar Farouq ta kasance tsohuwar ministar jin ƙai zamanin gwamnatin tsohon shugaban ƙasar, marigayi Muhammadu Buhari.

  10. Shugabar Mexico ta shiga muhawarar rufe makarantun ƙasar kan Gasar Kofin Duniya

    Shugabar ƙasar Mexico, Claudia Sheinbaum, ta shiga muhawarar da ministan ilimin ƙasar ya janyo a faɗin ƙasar, bayan da ya bayyana shirin gwamnatin ƙasar na kawo ƙarshen shekarar karatu da wuri, sakamkon gasar Kofin Duniya da za a buga a ƙasar da kuma yanyin hunturu da za a shiga.

    Kalaman ministan sun janyo martani daga iyayen yara da ƙungiyoyin malamai.

    Ms Sheinbaum ta ce ba a yanke hukuncin ƙarshe kan shawarar ma'ikatar ilimin ba.

    A ranar Alhamis ne ma'aikatar ilimin ta ce za a rage wata guda a shekarar karatun a watan Yuni.

    Tana mai cewa hakan zai sa a rage samun cunkoson ababen hawa a lokacin Gasar Kofin Duniya, da Mexico ke cikin masu ɗaukar nauyinta.

  11. Isra'ila ta nuna adawa da matsayin Pakistan na mai shiga tsakani a yaƙin Iran

    Isra'ila ta nuna rashin gamsuwarta ga rawar da Pakistan ke takawa ta mai shiga tsakani a ƙoƙarin kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Iran.

    Jakadan Isra'ila a Mumbai na ƙasar Indiya, Yaniv Revach, ya ce: "Ba na tunanin gwamnatin ƙasata na jin daɗin rawar da Pakistan ke takawa ta mai shiga tsakani a yaƙin Iran da Amurka.''

    Ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na ANI cewa ''Isra'ila ba ta yi wata tattaunawa da Pakistan ba.

    Shugaban Amurka Donald Trump ne ke jagorantar tattaunawar. Kuma na yi imanin cewa gwamnatin Amurka za ta kare muradin tsaron Isra'ila a wannan batu''.

    Shugaban na Amurka, Donald Trump da shugabannin Iran, duka sun gode wa Pakistan kan wannan matsayi nata na mai shiga tsakani.

    Duka ƙasashen biyu sun aika wakilansu zuwa Pakistan domin shiga tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin.

    Isra'ila dai ba ta aika kowa zuwa ganawar ba.

  12. Majalisar dokokin Iran za ta yi zamanta na farko tun bayan fara yaƙi

    Kamfanin dillancin labaran Iran IRNA ya ce majalisar dokokin Iran na zamanta na farko tun lokacin da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar da hare-hare kan Iran

    Kakakin majalisar Abbas Kodarzi ya ce a karon farko tun bayan fara yaƙin, majalisar za ta yi zamanta na farko ta bidiyo.

    Kodarzi ya ce za a yi zaman a gobe Lahadi bisa “matakan da aka ɗauka na amfani da bidiyo la'akari da halin da ƙasar ke ciki''.

    Ya ƙara da cewa a zaman na gobe, ƴan majalisar za su tattauna batutuwan da suka shafi tattalin arziki da damuwar da mutane suka shiga sakamakon yaƙin.

    Zama na ƙarshe da majalisar ta yi a zaurenta shi ne ranar 16 ga watan Fabrairun da ya gabata, da suka yi muhawara kan kasafin kuɗin ƙasar na wannan shekara.

  13. Muna jiran martanin Iran don cimma yarjejeniya - Trump

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya shaida wa masu aiko da rahotonni cewa yana sa ran samun martanin Iran nan ba da jimawa ba domin cimma yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin ƙasar.

    A ƴan kwanakin bayan nan an riƙa samun arangama tsakanin ɓangarorin biyu a ciki da kewayen mashigar Hormuz, wata guda tun bayan fara aiki da yarjejeniyar dakatar da wuta, haka ma an kai hari ƙasar UAE a ranar Juma'a.

    ''Amurka na jiran martanin Iran kan shawarar Amurka, wadda ta ƙuduri aniyar kawo ƙarshen yaƙin a hukumance kafin fara tattaunawa kan muhimman batutuwan, ciki har da da shirin nukiliyar Iran'', in ji shi.

    Iran ta zargi Amurka ta saɓa wa yarjejeniyar dakatar da wutar, wadda ta fara aiki tun ranar 7 ga watan Afrilu, kodayake a wannan mako an riƙa samun ƙaruwar matsin lamba da zaman ɗarɗar.

  14. Yarjejeniyar dakatar da wuta ta kwana uku tsakanin Rasha da Ukraine ta fara aiki

    An yi amanna cewa yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta ta tsawon kwana uku, wadda Shugaba Trump ya samar a tsakanin Rasha da Ukraine ta kankama.

    A yarjeniyoyin dakatar da buɗe wuta da aka yi a baya, sun ci gaba da yaƙi, inda kowane ɓangare ke zargin ɗayan da saɓawa.

    Daman an tsara za ta fara aiki ne a yau Asabar, ranar da Rasha za ta fara bikin tunawa da nasarar da ta samu ta murƙushe gwamnatin Jamus ta ƴan Nazi a Yakin Duniya na Biyu.

    Shugaba Zelensky na Ukraine ya umarci dakarunsa da kada su kai hari kan dandalin Red Square da ke Moscow - inda Rasha za ta yi babban faretin sojinta, duk da dai cewa a bana ba za a yi bikin sojin ba da manyan motocin yaƙi na igwa ko makamai masu linzami ba.

    A ƙarƙashin yarjejeniyar dakatar da buɗe wutar - ƙasashen biyu sun amince su yi musayar dubban fursunonin yaƙi.

  15. Sojojin Najeriya sun ce sun kashe mayaƙan ISWAP 50 a Yobe

    Sojojin Najeriya, ƙarƙashin rundunar Operation HADIN KAI mai yaƙi da Boko Haram ta ce dakarunta sun kashe mayaƙan ISWAP kusan 50 a wani gumurzu da mayaƙan ƙungiyar a Buni Gari da ke jihar Yobe.

    Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar Laftanal Kanal Sani Uba ya fitar ya ce lamarin ya faru ne a daren Juma'a, lokacin da maharan suka biyo duhun dare don ƙaddamar da mummunan hari kan shalkwatar sojoji ta 27 Brigade da ke Buni Gari.

    Sanarwar ta ce sojojin sun mayar da martani cikin ƙwarewa da ƙarfin makamai, lamarin da ya ba su damar fatattakar mayaƙan.

    Sani Uba ya ce mayaƙan sun karkasu zuwa gida uku, inda suka riƙa far wa shalkwatar a lokuta daban-daban, da nufin mamayeta da yi wa dakarun ƙawanya, amma sojojin suka turji tare da fatattakar mayaƙan cikin ƙwarewa.

    Sojojin sun ce dakarun ƙasan sun samu taimakon na sama, ta hanyar aika jirgi, da ya riƙa bin mayaƙan yana jefa musu bama-bamai, a lokacin da suke tserewa.

    Sanarwar ta kuma ce sojojin sun ƙwato makamai masu yawa, nau'ika daban-daban ciki har da nakiyoyi da makaman harba gurneti.

    Sai dai rundunar sojin ta ce biyu daga cikin dakarunta sun rasu a lokacin musayar wutar.

  16. Jirgin sama ya buge wani mutum a Amurka

    Fiye da fasinjoji 200 aka fitar daga wani jirgin sama a Amurka bayan da ya jirgin ya bugi wani mutum da ke tafiya a kan titin jirgin kafin tashinsa.

    Direban jirgin ya dakatar da shirin tashi bayan faruwar lamarin, sakamakon wutar da ta kama ɗaya daga cikin injunan jirgin.

    A wani saƙon murya da aka naɗa daga ɗakin kula da tashin jiragen an ji muryar direban jirgin na cewa injin jirgi ya kama da wuta.

    Kamfanin jirgin, Frontier, da ya mallaki jirgin ya ce ya kaɗu da faruwar lamarin, kuma tuni aka ƙaddamar da bincike.

  17. Starmer na fuskantar matsin lamba bayan jam'iyyarsa ta sha kaye a zaɓen Birtaniya

    Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, na ci gaba da fuskantar matsin lamba daga cikin jam'iyyarsa ta Labour kan ya sauka daga muƙaminsa, sakamakon shan kaye da jam'iyyar ta yi a zaɓukan ƙananan hukumomi da kansiloli a faɗin ƙasar a jiya Alhamis.

    A zaɓen ƙananan hukumomi a Ingila - dukkanin manyan jam'iyyun ƙasar biyu - Labour - mai mulki da kuma Conservative mai hamayya - sun yi rashin nasara sosai - galibi a hannun jam'iyyar Reform UK - mai ra'ayin riƙau.

    Haka kuma jam'iyyar ta Labour ta sha gagarumin kaye a zaɓukan majalisar dokokin yankin Wales.

    Can ma a yankin Scotland jam'iyyar National Party ce ta yi nasarar cin kujerun majalisar dokokin yankin fiye da kowace jam'iyya - kodayake ba ta samu rinjayen da take buƙata ba.

    Ƴan majalisar dokokin Labour fiye da 20 ne suka fito fili suna kiran ya sauka ko kuma ya sanya wani lokaci da zai ajiye muƙamin.

    To sai dai Mista Starmer ya yi watsi da kiran nasu, yana mai cewa ba zai sauka ba, inda ya alƙawarta shawo kan matsalolin da al'ummar ƙasar ke nuna damuwa a kansu.

  18. Amurka za ta shirya gagarumar tattaunawa tsakanin Isra'ila da Lebanon

    Amurka ta tabbatar cewa za ta shirya babbar tattaunawa ta tsawon kwana biyu tsakanin Isra'ila da Lebanon ranar Alhamis da Juma'a na mako mai zuwa.

    Ta ce ɓangarorin biyu za su tattauna ainun a kan samar da cikakkiyar yarjejeniyar zaman lafiya da tsaro.

    Har yanzu dai a hukumance akwai ƙwarya-ƙwaryar yarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu.

    To amma jami'an Lebanon sun ce hare-haren da Isra'ila ke kai wa a kudancin Lebanon ɗin sun hallaka mutum bakwai a jiya Juma'a kaɗai.

    Ita ma ƙungiyar Hezbollah da ke samun goyon bayan Iran ta ce ta ƙaddamar da hare-haren makamai masu linzami da na ƙananan jiragen sama marasa matuƙa a kan sansanonin sojin Isra'ila, domin ramuwar gayya a kan harin da Isra'ila ta kai Beirut ranar Laraba - wanda ya kashe daya daga cikin manyan kwamandojinta.

  19. An ga alamar malalar mai a tsibirin Kharg na Iran

    Hotunan tauraron ɗan'adam sun nuna wata malalar mai da ta kai ta faɗin murabba'in kilomita 50 a kusa da Tsibirin Kharg - babbar cibiyar samar da mai ta Iran.

    Ba a dai san takamaiman me ya haddasa malalar ba, da aka gani a gaɓar yamma ta tsibirin.

    Wata ƙungiya da ba ta gwamnati ba - mai lura da batutuwan rikici da kuma muhalli - The Conflict and Environment Observatory - ta ce alamu sun nuna cewa malalar ta yi kama da ta mai, kuma tana kwaranya ne zuwa kudanci.

    Tsibirin Kharg, nan ne Iran take da yawancin rijiyoyin mai da bututan man da tankunan ajiya da dai sauran kayayyaki na harkar manta.

  20. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye, barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku domin kawo muku halin da duniyar ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.