Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Alhamis 07/05/2026

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Aisha Aliyu Jaafar da Nabeela Mukhtar Uba

  1. An ceto sauran mutanen da aka sace daga gidan marayu a jihar Kogi

    Rundunar sojojin Najeriya ta ce dakarunta sun ceto yara bakwai da manya biyu da aka sace daga wani gidan marayu a jihar Kogi a watan da ya gabata.

    Cikin wata sanarwar da ta fitar, runduar sojin ta ce an ceto su ne a wani aiki da jami'an tsaro suka yi.

    Satar mutane domin neman kuɗin fansa dai ya zama ruwan dare a Arewa ta Tsakiyar Najeriya, inda ƴan bindiga ke yawaita kai hari kan makarantu da kuma ƙauyuka.

  2. Bello El-Rufai ya fice daga jamiyyar APC zuwa ADC

    Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kaduna ta Arewa a majalisar wakilan Najeriya Hon. Mohammed Bello El-Rufai ya sanar da sauya sheƙarsa daga jamiyyar APC mai mulki, zuwa Jamiyyar ADC.

    A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafukansa na sada zumuta, Bello El-Rufai ya kuma ce zai sake neman takarar kujerar ɗan majalisar wakilai a ƙarƙashin sabuwar jamiyyarsa.

    A cewar sa, matakin sauya sheƙar bai zo masa da sauƙi ba, sai dai a matsayinsa na ɗan tsohon gwamnan Kaduna Mallam Nasir El Rufai, yana cike da ƙwarin gwiwa, da jajircewa da kuma imanin cewa alummar jihar na buƙatar wakilci na gari da kuma ci gaba.

    Ya kuma ce ya koma jamiyyar ADC ne tare da ɗan majalisa mai wakiltar Soba Hon Engr Suleiman Richifa, da kuma na Makarfi/Kudan Hon Umar Ajilo.

  3. Gwamnatin Sokoto ta ce yara 33 sun mutu sakamakon ɓarkewar cutar sankarau

    Gwamnatin jihar Sokoto ta tabbatar da mutuwar yara 33 sakamakon ɓarkewar cutar sankarau a wasu sassan jihar.

    Kwamishinan lafiya na jihar Dr Faruk Abubakar, wanda ya tabbatar da hakan a jiya Laraba, kamar yadda jaridar DailyTrust ta ruwaito, ya ce tun bayan bullar cutar a watan da ya gabata, mutum 256 ne ake zargin sun kamu da ita a ƙananan hukumomi takwas na jihar.

    Dr Abubakar ya ce an samu mutum 63 da ake zargi sun kamu da cutar a ƙaramar hukumar Sabon Birni, sai mutum 60 a Wamakko, sai kuma mutum 51 a Shagari, a Tambuwal kuma an samu mutum 33, sai Dange Shuni mai mutum 26, a Kebbe kuma an samu 16, sai Bodinga da Kware an samu mutum biyu biyu, yayin da aka samu mutum ɗaya a Gada.

    Kwamishinan lafiyar ya ce akasarin waɗanda suka mutu saboda cutar, sun mutu ne a gida kafin a kai ga zuwa asibiti.

    Ya alaƙanta jinkirin da ake samu wajen kai marasa lafiya asibiti da mummunar fahimtar da ake yi cewa cutar aljanu ce ba ta asibiti ba.

  4. Kotu ta samu tsohon ministan lantarkin Najeriya da badaƙalar Naira biliyan 33

    Wata babbar kotun tarayya a Najeriya da ke Abuja, ta samu tsohon ministan lantarki Saleh Mamman da laifuka 12 da suka shafi halasta kuɗaɗen haram kimanin Naira biliyan 33.

    Mai shari'a James Omotosho, wanda ya yanke hukuncin a yau Alhamis, ya jinkirta yanke masa hukunci har sai ranar 13 ga watan Mayun 2026, kasancewar tsohon ministan ba ya kotun a lokacin da aka same shi da laifin.

    A cikin bayanin da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC ta wallafa a shafinta na sada zumunta, ta ce domin tabbatar da cewa bai fice daga ƙasar ba kafin nan, lauyanta Rotimi Oyedepo SAN, ya buƙaci kotun ta bayar da sammacin kawo tsohon ministan kotu.

    Saleh Mamman dai ya riƙe muƙamin minista ne daga shekarar 2019 zuwa 2021 ƙarƙashin gwamnatin marigayi tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

    A ranar 28 ga watan Afrilun wannan shekara ne kuma ya sayi fom ɗin neman takarar zama gwamna a jihar Taraba a ƙarƙashin jamiyyar APC mai mulki.

  5. Ta yaya tarwatsewar ƴan adawa zai shafi zaɓen 2027?

    A daidai lokacin da babban zaɓen Najeriya na shekarar 2027 ke ƙara ƙaratowa, masu bibiyar al'amuran siyasa na ganin salon na siyasar na ɗaukar salo daban-daban, musamman a ɓangaren ƴan hamayya.

    Tuni tsoffin ƴantakarar shugaban Najeriya biyu a zaɓen 2023 wato Rabiu Musa Kwankwaso da ya tsaya takara a NNPP a zaɓen 2023 da takwaransa na LP, Peter Obi suka dunƙule a sabuwar jam'iyyar NDC domin fafatawa da Bola Tinubu.

    Ƴantakarar biyu na cikin manyan jiga-jigan da a baya suka haɗu a jam'iyyar ADC da ake wa laƙabi da ta haɗaka, sabuwar haɗuwar manyan ƴan hamayya a cikinta domin fuskantar zaɓen 2027 a matsayin tsintsiya maɗaurinki ɗaya.

    A baya dai jam'iyyun hamayyar ƙasar sun gudanar da wani taron a birnin Badun na jihar Oyo domin samar da matsaya kan yadda za su fuskanci zaɓen, taron da ya samu halartar jiga-jigan PDP da ADC da Labour da NNPP.

  6. Ana ci gaba da neman wasu fasinjojin jirgin ruwan da aka samu ɓarkewar cutar HantaVirus

    Jami'an lafiya daga ƙasashe da dama na ci gaba da ƙoƙarin gano fasinjojin da suka bar wani jirgin ruwan yawon buɗe ido kafin a tabbatar da ɓarkewar cutar HantaVirus a cikinsa.

    Gwamnatin Netherlands ta ce ana nema fasinjoji aƙalla 40 da suka fice aga jirgin samfurin MV Hondius a tsibirin Saint Helena kafin a samu rahoton ɓarkewar cutar.

    Turawa uku ƴan yawon buɗe ido sun mutu sakamakon kamuwa da cutar, yayin da aka kwashe wasu da dama domin su sami kulawa a asibitoci da ke Turai da Africa ta Kudu.

    A yanzu jirgin ruwan na kan hanyarsa ta zuwa Tsibirin Canary da ke Sipaniya.

  7. Shugaban Sudan ta Kudu ya kori babban hafsan sojin ƙasar da ministan kuɗi

    Shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir ya kori babban hafsan sojojin ƙasar da ministan kuɗi a sauye sauye na baya bayan nan da ya yi a gwamnatinsa.

    Bai bayar da dalilin yin hakan ba, amma masu sharhi sun ce ya yi hakan ne da nufin ƙarfafa ikonshi a yayin da ake samun rashin tabbas kan magajin shi.

    Sudan ta kudu dai ta yi ta fama wajen aiwatar da sauye sauye da aka amince da su ƙarƙashin yarjejeniyar zaman lafiya ta 2018 wadda ta kawo ƙarshen yaƙin basasar shekaru biyar, ciki har da gudanar da zaɓuka.

    An ɗage zaɓe har sau uku, inda a yanzu aka shirya yi a watan Disamban wannan shekara, sai dai har yanzu babu tabbacin ko zaɓen zai gudana.

  8. Ana ci gaba da jimamin mutuwar mutumin da ya kafa gidan talibiji na CNN

    Ana ci gaba da aikewa da saƙonnin ta'aziyya bayan mutuwar Ted Turner, mutumin da ya kafa kamfanin da ya mallaki gidan talabijin na CNN, wanda ya rasu yana da shekara tamanin da bakwai.

    Shugaban Amurka Donald Trump, ya bayyana attajirin a matsayin "ɗaya daga cikin jiga-jigan da suka sauya fuskar yaɗa labarai a duniya.

    Goggagiyar mai gabatar da shirye-shirye a CNN Christiane Amanpour na cikin waɗanda suka aike da saƙon ta'aziyyarsu.

    Ta ce ''ya sauya duniya, Ted shi ne ya kirkiri gidan talabijin na farko da ya shiga ko ina a faɗin duniya da ya ke watsa shirye-shirye babu kakkautawa''.

    Baya ga CNN saran tashohin da Ted Turner ya mallaka sun hada da TNT sports da Cartoon Network da kuma Turner Classic Movies

  9. Wasu iyalai masu alaƙa da ƙungiyar IS sun koma Australiya bayan shafe shekaru a Syria

    Wasu iyalai da suka ƙunshi mata huɗu da yara 9 da ke da alaka da ƙungiyar masu ikirarin jihadi na Islamic State, sun isa Australia a yau, bayan shafe shekaru a wani sansani a Syria.

    Ƴan sandan Australia sun yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar za a kama wasu daga cikin matan a kuma tuhume su.

    Komawarsu Australia dai ya fuskanci adawa mai ƙarfi a siyasance, amma masu fafutuka na ganin bai kamata a hukunta yaran saboda abin da iyayensu suka aikata ba.

    Yaran da ake tunanin shekarun su sun kama ne daga shekara shida zuwa sama - za su sami tallafi ta fannin kula da lafiyar kwakwalwarsu da kuma sauya musu tunani don kar su kasance masu tsattsauran ra'ayi.

  10. An tabbatar wa wani sojan Italiya ɗaurin shekaru 20 saboda sayar wa Rasha bayanai

    Wata kotu a Italiya ta tabbatar da hukuncin ɗaurin shekara 20 da aka yanke wa wani tsohon jami'in sojan ruwan Italiya bisa laifin sayar da wasu bayanan sirri ga Rasha, inda ta ƙi amincewa da ɗaukaka ƙarar da ya shigar.

    An kama Walter Biot, wanda kyaftin ne a rundunar sojin ruwa, a wani wurin ajiye motoci a birnin Roma shekara biyar da suka gabata, inda ya mika takardun sirri na kungiyar tsaro ta NATO ga jami'an ofishin jakadancin Rasha bayan an biya shi kusan dala dubu shida.

    Biot dai ya na zaman gidan yari na shekara 30 bayan wani hukunci na daban da wata kotun soji ta yanke masa akan laifuka makamantan waɗannan da ake tuhumnarsa da su.

  11. Yaƙin da ake yi a Iran na dab da zuwa ƙarshe - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya yi hasashen cewa yaƙin da ake yi a Iran na dab da kawo ƙarshe, inda ya ce mutane da dama sun fahimci dalilinsa na kawo ƙarshen burin Tehran na mallakar nukiliya.

    Shugaba Trump ɗin ya kuma shaida wa manema labarai cewa Iran ta 'amince' ba za ta mallaki makamin nukiliya ba, wani abu da har yanzu Iran ɗin ba ta tabbatar ba.

    Kalamansa na zuwa ne a yayin da Iran ta ce tana nazari kan daftarin da Amurka ta gabatar.

    A wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban Faransa Emmanuel Macron, Shugaba Iran Masoud Pezeshkian ya ce ba za a cimma wata yarjejeniya ba har sai an bayar da tabbacin kawo ƙarshen yaƙin da kuma kawo ƙarshen toshe tashohin jiragen ruwa Iran.

    Rahotanni a kafafen yaɗa labaran Iran sun kuma ruwaito cewa an sake buɗe filin jirgin sama na Tabriz.

  12. Isra'ila ta kashe ɗaya daga cikin manyan kwamandojin Hezbollah a harin da ta kai Beirut

    Wata majiya da ke kusa da kungiyar Hezbollah ta shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa an kashe ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ta a wani harin da Isra'ila ta kai a kudancin birnin Beirut na kasar Labanon a jiya Laraba.

    Wannan dai shi ne hari na farko da aka kai a yankin cikin kusan wata guda.

    Majiyar ta bayyana sunan kwamandan a matsayin Malek Ballout, wanda aka ce shi ne kwamandan ayyuka na rundunar Radwan ta ƙungiyar.

    Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce shi da kan sa ya bayar da umarnin kai harin da aka kai kan kwamandan rundunar mayakan na Hezbollah.

  13. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafin BBC Hausa kai-tsaye, muna muku maraba da zuwa shafinmu na yau Alhamis.

    A yau ma, za mu kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a duniya, kama daga yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran, da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za kuma ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta kamar Facebook da Instagram da YouTube da kuma X domin kallon bidiyo da kuma tafka muhawara.